Kungiyar Hamas ta yi Allah-wadai da matakin hadin gwiwa da Amurka da Tarayyar Turai suka dauka na hana watsa tashar talabijin ta Al-Aqsa ta Larabci ta Falasdinu da ke da alaka da kungiyar gwagwarmayar.

Kungiyar ta bayyana hakan a matsayin wani yunkuri na toshe muryar Falasdinawa.

Sanarwar da Hamas ta fitar ta kara da cewa, wannan shawarar toshe ‘yancin watsa labaru ne da kuma hakki na al’ummar Falasdinu na a ji muryarsu a duniya.

Hamas ta yi kira ga cibiyoyin yada labarai na kasa da kasa da su yi Allah wadai da wannan shawarar, kuma kada su yi shiru dangane da cin zarafin da gwamnatin sahyoniya ta ke yi wa dokokin kasa da kasa da ka’idojin jin kai.

Bisa shawarar hadin gwiwa da Amurka da EU suka cimma, za a ci tarar duk wani sashe na tauraron dan adam da ke yada shirye shiryen tashar talabijin ta Al-Aqsa bisa zargin da ake mata na “yada ayyukan ta’addanci.”

Ita ma a nata bangaren, kungiyar Jihad Islami ta Falastinu ta yi tir da haramcin da aka yi wa tashar talabijin din ta Al-Aqsa, tana mai cewa wani hari ne da nufin murkushe muryar Falasdinu da kuma hana al’ummar kasar isar da sakonin ukubar da suke fuskanta ga duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe

Wani mummunan al’amari ya girgiza al’umma a Ƙaramar Hukumar Kwami, Jihar Gombe, inda ake zargin wani magidanci ya jagoranci sacewa da kashe ɗansa mai shekara shida domin yin tsafin kuɗi.

Ana zargin cewa mahaifin yaron shi ne jagoran kisan kuma Yana cikin waɗanda suka tsere, a yayin da hukumomi ke ci gaba da farautar sa.

Tuni ’yan sanda suka cafke mutane takwas bisa zargin wannan aika-aika a unguwar Bura-Bunga da ke ƙaramar hukumar.

Kakakin ’yan sanda a Jihar Gombe, DSP Buhari Abdullahi, ya sanar cewa waɗanda suka shiga hannu sun amsa cewa sun kashe yaron ne bisa umarnin bokaye da suka nemi sassan jikin ɗan Adam don yin tsafin kuɗi.

An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi ’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa 

Bincike ya nuna wani mai shekaru 45, wanda ake zargin shi ne shugaban gungun, ya hallaka yaron tare da raba sassan jikinsa gida biyu.

Ɓangaren sama na jikinsa an jefa shi cikin rijiyar, yayin da ɓangaren kasa aka bai wa abokan laifinsa.

Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu bokaye biyu ne suka nemi sassan jikin yaron, kuma wani matashi mai shekaru 18 ne ya sace yaron, sannan wani ya haɗa bokayen da su.

Kwamishinan ’yan sanda, CP Bello Yahaya, ya bayyana cewa za a tabbatar an gurfanar da duk masu hannu a wannan mummunan kisa a gaban ƙuliya.

Ya kuma yi kira ga jama’a su riƙa sa ido tare da bayar da rahoto kan duk wani abu mai kama da waɗanda ake nema jami’an tsaro.

Rundunar ’yan sanda ta jaddada aniyarta na kawo ƙarshen irin waɗannan munanan laifuka a faɗin jihar ta Gombe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Me Ke Sa Amare Yin Watsi Da Kwalliya Idan Sun Kwana Biyu A Gidan Miji?
  • Hamas Ta Yi Allawadai Da Dage Rigar Kariya Na Ma’aikatar Hukumar UNRWA
  • Sulhu da ’yan bindigar Katsina: Gaba aka ci ko baya?
  • Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
  • Tashin Gobara A Tashar Jirgi Ruwa Na Shahid Raja’i Da Ke Kudancin Iran Ya Jikkata Mutane Masu Yawa
  • Tashin Gobara A Tashar Jirgi Ruwa Na Shahid Raja’i Da Ke Kudancin Iran Ya Lashe Rayukan Mutane A Kudancin Iran
  • ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Sun Yi Kira Ga Kungiyoyin Kasa Da Kasa Da Su Ceto Yara Da Tsofaffi Daga Mummunan Kangi A Sudan
  • Rahoton Gwamnatin Amurka Game Da Shawo Kan Yaduwar Makamai Tamkar Ba’a Amurkan Ta Yiwa Kanta
  • Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)