HausaTv:
2025-03-16@01:45:16 GMT

Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna

Published: 15th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Tehran a shirye take ta shiga tattaunawa da kasashen Turai bisa mutunta juna.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Araghchi da Ministan Harkokin Wajen Netherlands Caspar Veldkamp sun tattauna hanyoyin inganta alakar juna da sabbin abubuwa dake faruwa a yankin da na kasa da kasa.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya nanata tsarin kasar na kulla kyakkyawar alaka ta diflomasiyya da kasashen.

Iran da kasashen Turai dai na tattaunawar ba-zata kai a kai tun shekara ta 2021, shekaru uku bayan da Amurka ta fice daga yarjejeniyar nukiliyar iran – tare da maido da takunkumin da Washington ta kakaba wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

bangarorin kasashen Turai da suka shiga yarjejeniyar nukiliya – Birtaniya, Faransa da Jamus – sun kasa cika alkawarin da suka dauka na dawo da Washington cikin yarjejeniyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Pakistan Ta Zargi Kasashen Afghanistan Da India Da Hannu A Garkuwa Da Jirgin Kasa Na Sojoji

Gwamnatin kasar Pakistan ta ce da akwai hannuwan Afghanistan da kuma India a  garkuwa da jirgin kasa na soja da aka yi a cikin kasar a ranar 13 ga watan Maris,wanda ya jefa mutanen kasar cikin damuwa akan batun tsaro.

Mahukuntan kasar ta Pakistan sun kuma ce; Binciken farko ya tabbatar da cewa wasu masu dauke da makamai ne su ka yi garkuwa da jirgin kasar,  da sun shigo ne daga iyakar Pakistan sai kuma wani dan India wanda ya shiya yadda za a yi.

Gwamnatin kasar ta Pakistan ta sanar da tsananta matakan tsaro domin kame wadanda su ka yi garkuwa da jirgin da kuma daukar matakan hana, irin haka faruwa a nan gaba.

Ya zuwa yanzu babu wata kungiyar da ta fito fili ta dauki alhakin abinda ya faru.

Gwamnatin kasar ta Pakistan ta ce, da akwai masu dauke makamai da sun kai 50 da suke garkuwa da jirgin kasan. Ya zuwa yanzu dai mutane 31 ne su ka rasa rayukansu da usn kunshi jami’an tsaro da kuma fararen hula.

A cikin shekarun bayan nan alaka a tsakanin Pakistan da Afghanistan ta kara kamari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Pakistan Ta Zargi Kasashen Afghanistan Da India Da Hannu A Garkuwa Da Jirgin Kasa Na Sojoji
  • Kasashen Sin, Rasha Da Iran Sun Yi Kira Da Dakatar Da Matakin Kakaba Takunkumi Na Bangare Guda
  • Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Warware Batun Nukiliyar Iran
  • Taron Kasashen Iran, Rasha Da China A Birnin Beijing Ya Bukaci A Kawo Karshen Takunkumai Akan Tehran
  • Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta
  • Me Ya Sa Jama’ar Turai Ke Adawa Da Sayen Kayayyaki Kirar Amurka?
  • Sojojin Iran Sun Ce A Shirye Suke Su Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana Ga Tsaron Kasar
  • Jagora : kiran Trump, na tattaunawa Da Iran yaudarar duniya ne
  • Rasha  na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran