HausaTv:
2025-03-17@05:19:32 GMT

Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna

Published: 15th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Tehran a shirye take ta shiga tattaunawa da kasashen Turai bisa mutunta juna.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Araghchi da Ministan Harkokin Wajen Netherlands Caspar Veldkamp sun tattauna hanyoyin inganta alakar juna da sabbin abubuwa dake faruwa a yankin da na kasa da kasa.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya nanata tsarin kasar na kulla kyakkyawar alaka ta diflomasiyya da kasashen.

Iran da kasashen Turai dai na tattaunawar ba-zata kai a kai tun shekara ta 2021, shekaru uku bayan da Amurka ta fice daga yarjejeniyar nukiliyar iran – tare da maido da takunkumin da Washington ta kakaba wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

bangarorin kasashen Turai da suka shiga yarjejeniyar nukiliya – Birtaniya, Faransa da Jamus – sun kasa cika alkawarin da suka dauka na dawo da Washington cikin yarjejeniyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Tir Da HKI Da Kokarin Wanke Kanta Tare Da Rabawa Addinin Musulunci Ta’addanci

Jakadan JMI na din din din a MDD Amir Saeed Iravani ya yi tir da HKI kan yadda take amfani da Kalmar “ta’addancin Addinin musulunci’ don rabawa addinin ayyukan ta’addanci.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Iravani yana fadar haka, a taron yaki da kin addinin musulunci a kasashen yamma da kuma kasashen da suke fama da karancin sanin addinin musulunci a duniya.

Iravani ya kara da cewa, shekaru uku da suka gabata ne babban zauren MDD ya samar da kuduri mai lamba 73/254 don yaki da kin musulmi da addinin musulunci a duniya. Jakadan ya yi tir da Banyamin Natanyahu Firai ministan HKI da yawan amfani da kalmomi wadanda suke rabawa addinin musulunci ayyukan ta’addanci.

A jiya Jumma\a 14 ga watan Maris na ko wace shekara ne Majalisar ta ware a matsayin ranar yaki da kin addinin musulunci ta duniya.

Iranawani ya bayyana cewa kasashen Turai da daman a da hannu a cikin kokarin raba ayyukan ta’addanci ga addinin musulunci, tare da kafa dokokin wadanda suke bawa wasu damar wulakanta addinai da kona littafansu masu tsarki saboda cusa gaba da kiyyar addinin musulunci da musulmi ga mutanen kasashen su. Da sunan yencin fadin al-barkacin baki.

Daga karshe jakadan ya bukaci kasashen duniya su kakkafa dokoki a kasashensu wadanda zasu bukaci zaman lafiya da mabiya ko wani addini a duniya da kuma kaucewa duk wanda rikicin saboda bambancin addini da kuma nuna wariya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kofar JMI A Bude Take Don Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Iran Tace: Amurka Bata Da Hakkin Tsara Mana Yadda Zamu Tafiyar Da Kasar Mu
  •  Pakistan Ta Zargi Kasashen Afghanistan Da India Da Hannu A Garkuwa Da Jirgin Kasa Na Sojoji
  • Iran Ta Yi Tir Da HKI Da Kokarin Wanke Kanta Tare Da Rabawa Addinin Musulunci Ta’addanci
  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  • Kasashen Sin, Rasha Da Iran Sun Yi Kira Da Dakatar Da Matakin Kakaba Takunkumi Na Bangare Guda
  • Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Warware Batun Nukiliyar Iran
  • Taron Kasashen Iran, Rasha Da China A Birnin Beijing Ya Bukaci A Kawo Karshen Takunkumai Akan Tehran
  • Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta