Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya nada tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, a matsayin mai ba shi shawara ta musamman, kuma mai kula da shirin samar da sauyi a fannin kiwo.

Bayo Onanuga, mai magana da yawun shugaban kasa, ya tabbatar da nadin na Jega a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a da ta wuce.

Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan NPA Za Ta Yunkuro Don Zamanantar Da Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya – Dantsoho

Sanawar ta ce, Tinubu ya yi fatan nadin na Jega, zai kawo ci gaba a harkar noma da kiwo, tare da karfafa yunkurin raya kasar.

Kafin wannan nadin na Jega, ya kasance mataimakin shugaban kwamitin shugaban kasa kan samar da sauyi a bangaren noma da kiwo tare da shugaban kasar Bola Tinubu.
Kazalika, kwamitin ya gabatar da shawarwari masu muhimmanci kan yadda za a inganta fannin aikin noma da kiwo da kuma kafa ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Majalisar dokokin jihar Kano ta wanke Arc. Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.

 

 

A yayin aikin tantance kwamishinonin, ya jaddada mahimmancin kiyaye babban tsarin ga birane da yankunan karkara.

 

Ya kuma yi alkawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke nauyin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora masa.

 

Adamu wanda a baya ya taba rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tsare-Tsare Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), ya bayyana jin dadinsa ga majalisar a yayin zaman majalisar.

 

Shugaban majalisar Jibril Ismail Falgore ya bukaci Adamu da ya kara samun nasarori a KNUPDA tare da yi masa fatan Alheri a sabon mukaminsa.

 

Nadin Adamu ya yi daidai da ikon da tsarin mulki na Gwamna Yusuf ya ba shi na nada ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.

 

KHADIJAH ALIYU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Ba Jakadan Afirka ta Kudu Sa’o’i 72 Ya fice daga kasar
  •  Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
  • ’Yan Adawa Na Kitsa Makarkashiyar Tsige Ni – Akpabio
  • Mutane 7 Sun Mutu, Kadarorin Miliyan 50.3 Sun Salwanta Dalilin Gobara A Kano
  • ‘An Kwashe Shekaru Ana Kashe Kudaden Yaran da ba a ma Haife su ba a Nijeriya’
  • Gidauniyata Za Ta Ci Gaba Da Tallafawa Matasan Jihar Sakkwato – Seyi Tinubu
  • Ƙasar Sin Ta Yi Alƙawarin Ƙarfafa Hulɗar Da Ke Tsakaninta Da Kano
  • Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Karfafa Huldar Dake Tsakaninta Da Kano
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina