Leadership News Hausa:
2025-03-16@01:42:49 GMT

Sakamakon Neman ’Yancin Taiwan Zai Kai Yankin Ga Halaka

Published: 15th, March 2025 GMT

Sakamakon Neman ’Yancin Taiwan Zai Kai Yankin Ga Halaka

A baya-bayan nan, jagoran ‘yan awaren Taiwan Lai Ching-te, wanda ya kira kansa da “mai rajin neman ‘yancin kan Taiwan”, ya kara ikirarin cewa bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan ba sa karkashin ikon juna, har ma ya ce wai Taiwan wata kasar demokradiyya ce mai mulkin kanta. Amma duk yunkurin Lai Ching-te ba zai iya canza gaskiyar da duniya ta amince da ita ba, wato Taiwan ba ta taba zama kasa ba, kuma ba za ta taba zama ba a nan gaba.

Sunan yankin Taiwa a MDD shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”. Manufar Sin daya tak a duniya ra’ayin bai daya ne na al’ummomin duniya, kuma bisa ka’idar ne kasashe 183 suka kulla huldar diflomasiya da Sin.

Ta yaya za a warware batun Taiwan? Tuni dai babban yankin kasar Sin ya tabbatar da cewa, a shirye yake ya yi iyakacin kokari da sahihiyar zuciya domin neman kyakkyawar makomar dinkewar kasar Sin cikin lumana. Amma idan ‘yan aware masu neman “’yancin Taiwan” suka yi tsokana ko tilasta neman ballewa ko ma tabo batu mai tada kura, dole ne zai dauki matakai masu tsauri. Lai Ching-de da mabiyansa da ke wasa da wuta a mashigin tekun Taiwan, za su kone kansu. Sin za ta hada yankunanta, kuma tabbas za su dunkule. Wannan shi ne yanayin tarihi da ba za a iya juyawa ba. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Firaministan Lebanon: Rashin Fahimta Da Shakku Daga Waje Ba Za Su Iya Dakatar Da Ci Gaban Kasar Sin Ba

Daga ranar 2 zuwa 4 ga watan Disamban shekarar 2024, an gudanar da taron kasa da kasa na “Fahimtar kasar Sin” a birnin Guangzhou. A yayin taron, fiye da baki 600 na kasar Sin da kasashen waje, ciki har da tsohon firaministan kasar Lebanon Hassan Diab, sun hallara don tattaunawa da yin musayar ra’ayi kan taken “Yin gyare-gyare-zamanintarwa irin ta kasar Sin da sabbin damammakin ci gaban duniya”, inda suka samu ra’ayin bai daya na gudanar da hadin gwiwa. A tattaunawar da ya yi da wakiliyar babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin, wato CMG a takaice, Hassan Diab ya bayyana cewa, fahimtar kasar Sin yana da matukar muhimmanci, domin kasar na bude kofarta ga duniya.

A cikin ‘yan shekarun nan, an samu rashin fahimta, shakku har ma da suka game da ci gaban da kasar Sin ta samu cikin lumana, da tasirinta a duniya. Dangane da haka, Diab ya ce, duk wadannan ba za su hana kasar Sin samun ci gaba a fagen duniya ba. Ya ce, wadanda ba sa son ganin yadda kasar Sin ke kara cimma nasara, suna bukatar karfafa hulda da jama’ar kasar don kara fahimtar kasar. Kuma ya zama dole su amince da gaskiyar cewa kasar Sin ta bunkasa har ta zamanto babbar kasa a duniya a matakai da yawa, kuma kasar Sin na taka muhimmiyar rawa a yayin tabbatar da bunkasuwar kasashe daban daban a duniya. Ya kara da cewa, kamata ya yi su yarda tare da fahimtar hakan cikin natsuwa tare da gina wata gadar tuntubar juna da Sin. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Firaministan Lebanon: Rashin Fahimta Da Shakku Daga Waje Ba Za Su Iya Dakatar Da Ci Gaban Kasar Sin Ba
  • ’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina
  • Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 
  • Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba
  • Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Warware Batun Nukiliyar Iran
  • An Cire Maguire Cikin Tawagar Ingila Da Za Ta Buga Wasan Neman Gurbi
  • 2027: An Buga Gangar Neman Tazarcen Tinubu A Arewa
  • Kasar Sin Ce Ke Kan Gaba A Matsayin Kasar Da Ta Fi Samun Jari Daga Ketare
  • Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu – Obasanjo