Aminiya:
2025-03-17@06:26:10 GMT

Nijar ta kori wasu kamfanonin China 3 daga ƙasar

Published: 15th, March 2025 GMT

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta kori manyan jami’an wasu kamfanonin CNPC da WAPCO da SORAZ na China daga ƙasar.

Haka nan, gwamnatin ta kuma soke lasisin wani babban Otel na China da ke birnin Yamai.

Faɗuwar farashin kayan abinci a watan azumi ta shammace mu – ‘Yan kasuwa ’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina

Gwamnatin Nijar ɗin na zargin kamfanonin da ƙin mutunta dokokin aiki a ƙasar da ma na yarjejeniyar aiki da suka sanya wa hannu.

Wasu majiyoyi na kusa da gwamnatin sun tabbatar da cewa tun a ranar Larabar da ta gabata Shugaba Janar Abdourahmane Tchiani ya bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga manyan daraktacin kamfanonin CNPC mai aikin haƙar man fetur a Nijar da na kamfanin WAPCO da ke kula da jigilar ɗanyen man Nijar ta bututu zuwa tashar ruwan Cotonou da kuma na babbar matatar mai ta SORAZ su bar ƙasar baki ɗaya.

Majiyoyi na cewa hukumomin ƙasar ta Nijar na zargin kamfanonin na Chinar da aikata laifuka daban-daban da suka haɗa da ƙin mutunta yarjejniyar horas da ma’aikata ‘yan Nijar.

Haka kuma, hukumomin na zargin ci da gumin ma’aikatan Nijar ta hanyar ba su albashin da bai taka kara ya karya ba a gaban takwarorinsu na Chinar da ma shirya makarkashiyar da ta haddasa matsalar karancin man fetur a baya bayan nan a kasar.

Yanzu haka dai ko baya ga korar waɗannan manyan daraktoci na ƙasar China, gwamnatin mulkin sojan Nijar ta kuma sanar da ƙwace lasisin aiki na babban Hotel na SOLUXE mallakar China da ke birnin Yamai.

A ɓangaren ɗaya kuma Gwamnatin Nijar ɗin ta ba da izinin rufe asusun ajiyar kuɗi na babbar matatar mai ta kasa ta SORAZ.

Kawo yanzu dai kasar ta China ba ce uffan ba, haka kuma mahukuntan kamfanonin da abin ya shafa da aka tuntuɓa ba su magantu a kan lamarin ba.

A shekarar da gabata ce Nijar ta ƙulla yarjejeniyar cefanar da ɗanyen man fetur ta dala miliyan 400 da ake haƙowa a ƙasar.

A yayin da wasu ‘yan Nijar ke yaba wa da matakin wasu na ganinsa a matsayin barazana ga makomar hulɗar ƙasar da China da ma tattalin arzikin Nijar ɗin baki ɗaya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijar SORAZ WAPCO

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin Bana: NAHCON Za Ta Fara Jigilar Maniyyata A Ranar 6 Ga Mayu

“Muna kokarin kawar da bangaren dala. Abin da muke so mu yi shi ne mu biya a cikin kudin gida na duk kamfanonin jiragen sama. Kuma za a biya kudin ne daidai da farashin dala a halin yanzu a lokacin da ake biya.
“Kason da ya dace ya ba ku damar gudanar da ayyukanku dukkan ne za a biya ku, bayan kammala aikin za a karasa biyanku sauran,” ya shaida.

Tun da farko, shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Usman Saleh, ya ce, ayyukan jirage na sufuri na daga cikin muhimman ayyukan da ke gabansu wajen sauke nauyin aikin hajji.
“Lamarin na bukatar kwarewa matuka gaya da kuma himma da azama. Wannan lamarin ba kawai ga batun sufuri ba ne, ya shafi har da ciki alkawuran da aka dauka da mutuntaka da kariya hadi da saukaka wa maniyyata.”

Ya ce kamfanonin jiragen sama da aka yi aikin sun gudanar da cikakken tsarin zabe bisa cancanta, amintacce da kuma ingantaccen aiki.

“NAHCON ta yi taka-tsan-tsan wajen tabbatar da cewa kamfanonin jiragen sama masu inganci, ingantattun kayan aiki da fasinja ne kadai aka damka wa wannan gagarumin aiki.
“Kwarewarku da tarihinku na gudanar da manyan ayyuka, musamman ayyukan da suka shafi aikin hajji, sun ba mu kwarin gwiwa kan iyawar ku na gudanar da jigilar hajji cikin sauki.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka Ta Kudu Ta Caccaki Amurka Kan Korar Jakadanta Daga Washington
  • Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka
  • Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci 
  • Nageriya ta Maida Martani Kan Zargin Kissin Kiristoce A Kasar,Wanada Gwamnatin Amurka Ta Yi Mata
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya
  • Hajjin Bana: NAHCON Za Ta Fara Jigilar Maniyyata A Ranar 6 Ga Mayu
  • Karancin Man Fetur A Jamhuriyar Nijar Yana Damun ‘Yan Kasa
  • Taron Kasashen Iran, Rasha Da China A Birnin Beijing Ya Bukaci A Kawo Karshen Takunkumai Akan Tehran