Aminiya:
2025-04-14@16:36:47 GMT

Nijar ta kori wasu kamfanonin China 3 daga ƙasar

Published: 15th, March 2025 GMT

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta kori manyan jami’an wasu kamfanonin CNPC da WAPCO da SORAZ na China daga ƙasar.

Haka nan, gwamnatin ta kuma soke lasisin wani babban Otel na China da ke birnin Yamai.

Faɗuwar farashin kayan abinci a watan azumi ta shammace mu – ‘Yan kasuwa ’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina

Gwamnatin Nijar ɗin na zargin kamfanonin da ƙin mutunta dokokin aiki a ƙasar da ma na yarjejeniyar aiki da suka sanya wa hannu.

Wasu majiyoyi na kusa da gwamnatin sun tabbatar da cewa tun a ranar Larabar da ta gabata Shugaba Janar Abdourahmane Tchiani ya bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga manyan daraktacin kamfanonin CNPC mai aikin haƙar man fetur a Nijar da na kamfanin WAPCO da ke kula da jigilar ɗanyen man Nijar ta bututu zuwa tashar ruwan Cotonou da kuma na babbar matatar mai ta SORAZ su bar ƙasar baki ɗaya.

Majiyoyi na cewa hukumomin ƙasar ta Nijar na zargin kamfanonin na Chinar da aikata laifuka daban-daban da suka haɗa da ƙin mutunta yarjejniyar horas da ma’aikata ‘yan Nijar.

Haka kuma, hukumomin na zargin ci da gumin ma’aikatan Nijar ta hanyar ba su albashin da bai taka kara ya karya ba a gaban takwarorinsu na Chinar da ma shirya makarkashiyar da ta haddasa matsalar karancin man fetur a baya bayan nan a kasar.

Yanzu haka dai ko baya ga korar waɗannan manyan daraktoci na ƙasar China, gwamnatin mulkin sojan Nijar ta kuma sanar da ƙwace lasisin aiki na babban Hotel na SOLUXE mallakar China da ke birnin Yamai.

A ɓangaren ɗaya kuma Gwamnatin Nijar ɗin ta ba da izinin rufe asusun ajiyar kuɗi na babbar matatar mai ta kasa ta SORAZ.

Kawo yanzu dai kasar ta China ba ce uffan ba, haka kuma mahukuntan kamfanonin da abin ya shafa da aka tuntuɓa ba su magantu a kan lamarin ba.

A shekarar da gabata ce Nijar ta ƙulla yarjejeniyar cefanar da ɗanyen man fetur ta dala miliyan 400 da ake haƙowa a ƙasar.

A yayin da wasu ‘yan Nijar ke yaba wa da matakin wasu na ganinsa a matsayin barazana ga makomar hulɗar ƙasar da China da ma tattalin arzikin Nijar ɗin baki ɗaya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijar SORAZ WAPCO

এছাড়াও পড়ুন:

An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo

Jami’an tsaron Jihar Edo sun sake kama wasu mafarauta hudu daga Kano, makonni kadan bayan kisan gilla da ’yan bangar Jihar Edo suka yi wa ayarin wasu mafarauta 16 daga jihar Kano a jihar.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Edo, ta ce mafarautan da aka kama sun fito ne daga Karamar Hukumar Doguwa ta Jihar Kano, kuma suna dauke da bindigogin toka guda uku, da adduna da wukake a lokacin da aka kama su.

Kakakin ’yan sanda an jihar, CSP Moses Yamu, ya ce kanawan da aka kama mafarauta ne ba kamar yadda ake yadawa a kafofin sada zumunta cewa makiyaya ba ne.

Ya bayyana cewa jami’an kungiyar tsaro ta Jhar Edo ne suka kama mafarautan sannan suka damka su ga ’yan sanda inda ake yi musu tambayoyi a ofishin ’yan sanda da ke yankin Ikpoba Hill.

’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu

Ya ce an, “An kama mafarautan da suka fito daga Karamar Hukumar Doguwa ta Jihar Kano a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa yankin Uvbe da ke Karamar Hukumar Orhionwon a Jihar Edo. A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike.”

Da haka Kwamishinan ’yan sandan jihar, Monday Agbonika, ya gargadi jama’ar jihar da su guji yada abin da ba gaskiya ba ne game da lamarin, domin yana iya tayar da zaune tsaye.

Idan ba a manta ba, a cikin watan Ramadan, gab Sallah Karama ne ’yan banga suka yi wa wasu mafarauta 16 daga Jihar Kano da ke hanyarsu ta komawa gida hutun sallah kisan gilla a yankin Uromi da ke jihar, lamarin da ya haifar da tayar da jijiyoyin wuya, inda har yanzu ake kokarin shawo kansa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina
  • Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi