Daga ranar 2 zuwa 4 ga watan Disamban shekarar 2024, an gudanar da taron kasa da kasa na “Fahimtar kasar Sin” a birnin Guangzhou. A yayin taron, fiye da baki 600 na kasar Sin da kasashen waje, ciki har da tsohon firaministan kasar Lebanon Hassan Diab, sun hallara don tattaunawa da yin musayar ra’ayi kan taken “Yin gyare-gyare-zamanintarwa irin ta kasar Sin da sabbin damammakin ci gaban duniya”, inda suka samu ra’ayin bai daya na gudanar da hadin gwiwa.

A tattaunawar da ya yi da wakiliyar babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin, wato CMG a takaice, Hassan Diab ya bayyana cewa, fahimtar kasar Sin yana da matukar muhimmanci, domin kasar na bude kofarta ga duniya.

A cikin ‘yan shekarun nan, an samu rashin fahimta, shakku har ma da suka game da ci gaban da kasar Sin ta samu cikin lumana, da tasirinta a duniya. Dangane da haka, Diab ya ce, duk wadannan ba za su hana kasar Sin samun ci gaba a fagen duniya ba. Ya ce, wadanda ba sa son ganin yadda kasar Sin ke kara cimma nasara, suna bukatar karfafa hulda da jama’ar kasar don kara fahimtar kasar. Kuma ya zama dole su amince da gaskiyar cewa kasar Sin ta bunkasa har ta zamanto babbar kasa a duniya a matakai da yawa, kuma kasar Sin na taka muhimmiyar rawa a yayin tabbatar da bunkasuwar kasashe daban daban a duniya. Ya kara da cewa, kamata ya yi su yarda tare da fahimtar hakan cikin natsuwa tare da gina wata gadar tuntubar juna da Sin. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]

Mataki na Uku: Kare kai daga shubuha; wato matakin tsantseni, shubuha na nufin abubuwan da ba a tabbatar da halacci ko haramcinsu ba. Akwai wani mataki da ya fi kauce wa haram, wato kauce wa abubuwan da ke da shakku. Annabi (SAW) ya ce:
” Lalle halal a bayyane take, kuma lalle haram a bayyane yake, amma akwai wasu abubuwa masu rikitarwa a tsakanin su waɗanda mutane da yawa ba su san su ba, wanda ya nisanci shubuha, to ya kare addininsa da mutuncinsa.” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito. Saboda haka, matakin tsantseni yana nufin mutum ya kiyaye kansa daga duk wani abu da zai iya kai shi ga haram, koda kuwa ba a tabbatar da haramcinsa ba.

Mataki na Huɗu: Kare kai daga abubuwan da aka halatta; wato matakin gudun duniya. Wannan matakin ya fi zurfi domin yana nuni da zuhudu (wato yin watsi da son duniya). Duk da cewa akwai halal da aka ba wa mutum damar amfani da su, sai dai matakin mafi girman taƙawa shi ne rage kwaɗayin duniya domin kauce wa duk wani abu da zai shagaltar da mutum daga bautar Allah. Wannan ya dace da hadisin Annabi (SAW) da ya ce: “Ka kasance a duniya kamar baƙo, ko kuma kamar wani matafiyi.” Bukhari ne ya ruwaito. Don haka, matakin gudun duniya yana nuna cewa taƙawa ta gaskiya ba kawai da nisantar haram ba ce, har ma da rage dogaro da duniya don samun kyakkyawan sakamako a lahira.

Mataki na Biyar: Kare zuciya daga duk wani abu da ba Allah ba. Wato matakin bautar Allah kamar kana ganin Sa. Wannan shi ne matakin ihsani wanda Annabi (SAW) ya bayyana a hadisin Jibrilu da cewa:
“Ihsan shi ne ka bauta wa Allah kamar kana ganin Sa, idan ba ka ganin Sa, to Shi yana ganin ka.” Muslim ne ya ruwaito. Wannan matakin yana nuna tsarkake zuciya daga kowanne abu da zai shagaltar da mutum daga Allah. Ana son mai taƙawa ya kasance zuciyarsa a koyaushe a tare da Allah, yana ƙaunar Sa fiye da komai. Wannan matakin ne mafi girma a taƙawa, domin yana nuni da mutum ya kasance kullum yana jin tsoron Allah tare da ƙaunar Sa, ba wai kawai yana gudun azabarsa ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]
  • Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (3)
  • Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza
  •  Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14
  • NPA Za Ta Yunkuro Don Zamanantar Da Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya – Dantsoho
  • Mutane 7 Sun Mutu, Kadarorin Miliyan 50.3 Sun Salwanta Dalilin Gobara A Kano
  • Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Ta A Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya