Leadership News Hausa:
2025-03-16@18:29:05 GMT

Jami’ar Gwamnatin Tarayya Kachia Ta Shirya Tsaf Domin Fara Aiki

Published: 16th, March 2025 GMT

Jami’ar Gwamnatin Tarayya Kachia Ta Shirya Tsaf Domin Fara Aiki

Ya kara bayanin cewar Jami’ar za ta dauki sahun dalibanta na farko wato shekarar karatu ta 2025, inda ya kara jaddada aniyar gwamnati ta bada damar samun yin karatu na ilimi mai zurfi tare da bunkasa shi.

Ministan har ila yau ya ce zai taimaka wajen tabbatar da cewar Jami’ar ta samu nata kason daga Hukumar kula da ilimin manyan makaratun ta kasa, domin hakan zai taimakawa bunkasa Jami’ar cikin wani lokaci nan gaba.

Ya ci gaban da bayanin “Zan tabbatar da cewar Jami’ar ta samu taimako na gidauniya kula da ilimi mai zurfi ta lamurran manyan makarantu ta samun kudade daga wurinta wannan shekarar. Don haka wannan rana ce ta farin ciki ga al’ummar Kudancin Kaduna, al’ummar Jihar Kaduna, da kuma al’ummar Nijeriya baki daya kamar yadda ya furta maganar,” .

Da yake an mika satifiket din mallakar filin yanzu Gwamnatin tarayya c eke da mallakin filin da kuma Jami’ar, hakan kuma ya bada wata damar fara aikinta a Hukumance. “Filin yana da hekta fiye da 200 wanda yanzu Gwamnatin Jihar Kaduna ta mallakawa Gwamnatin tarayya ta hanyar ma’aikatar ilimi ta tarayya.Yanzu mune muke da takardar satifiket na mallakar Jami’ar,”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

IRGC: Iran ba za ta fara yaki ba amma za ta mayar da martani ga duk wata barazana

Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya yi gargadin cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta taba neman wata kasa da yaki ba, amma kuma  a lokaci guda ta shirya tsaf domin mayar da mummunan martani ga duk wata barazana ko shishigi daga makiya.

Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne a wannan Lahadi, bayan da Washington ta zargi Tehran da taimakawa sojojin Yaman a hare-haren da suka rika kaiwa haramtacciyar kasar Isra’ila a baya-bayan nan tare da yin kira da ta daina yin wanann zargi maras tushe balantana makama.

Salami ya ce, “Iran ba za ta taba zama mai fara yaki ba, amma idan aka fuskanci barazana, za ta mayar da martani mai tsanani.”

Shugaban kasar Amurka ya sake alakanta ayyukan da kungiyar Ansarullah ta Yaman ga Iran, ya kuma ce dole ne Iran ta daina  goyon bayan kungiyar mai gwagwarmaya.”

Salami ya jaddada cewa, mutanen Yemen al’umma ce mai ‘yanci da ke bin manufofi na kashin kansu ba tare da an yi musu katsalandan ba. In ji babban kwamandan na IRGC.

Salami ya jaddada cewa, “Mu ba al’ummar da ke gudanar da ayyukanta cikin sirri ba ne; a maimakon haka, muna yin komai a bisa doka da oda da kuma kiyaye ka’idoji na duniya, kuma komai namua  fili yake, kuma lokacin da muka dauki matakin soji a kan Isra’ila ba mu boye ma kowa ba kamar yadda duniya ta sheda hakan a cewar janar Salami.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • IRGC: Iran ba za ta fara yaki ba amma za ta mayar da martani ga duk wata barazana
  • Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen
  • Jajircewa Ce Sirrin Samun Daukakata A Masana’antar Kannywood -Sadik Sani Sadik
  •  Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14
  • Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci 
  • Wata Rana Za A Yi Wa Gwamnatin Tinubu Sambarka – Minista 
  • Rasha ta caccaki gwamnatin Syria dangane da kisan kiyashin da jami’anta suke yi a kan tsiraru
  • Ƙasar Sin Ta Yi Alƙawarin Ƙarfafa Hulɗar Da Ke Tsakaninta Da Kano
  • Matsalar Tsaro: Shugaban Ƙaramar Hukuma ya tabbatar da haɗa kai da Sarakuna