Soja ya shafe mako guda da harsashi a cikin ƙwaƙwalwarsa
Published: 16th, March 2025 GMT
Kafofin yada labaran kasar Rasha sun yi ta jinjina wa wani sojan kasar a matsayin jarumi saboda ci gaba da fafatawa a yankin Kursk tsawon mako guda bayan harbin da aka yi masa a ka.
Mutumin da ba a bayyana sunansa ba, wanda aka ruwaito cewa yana cikin Brigade na 155 na Marine na Rukunin Pacific Fleet na Rasha, ya ci gaba fafatawa da sojojin Ukraine a Kursk lokacin da aka harbe shi.
A lokacin an harbi hular kansa, amma yana tunanin tabbas harsashin ya huda cikinta.
Ya samu kumburi a saman idonsa, wanda daga ƙarshe ya sa idonsa ya fara rufewa, amma sai kawai ya ci gaba da harkokinsa, yana tunanin kumburin zai warke da kansa.
Sai dai bayan wani rauni da ya samu mai alaka da rauni ne ya sa sojan ya ziyarci asibiti, inda ya samu labarin cewa harsashin da ya soki kwakwarsa ya huda kokon kansa ya shiga kwakwalwarsa.
Hotunan sojan sun nuna ya samu mummunan rauni a wani wuri da harsashi ya ragargaza hularsa, inda gefan idonsa daya ya kumbura, amma ba a san yadda shi ko sauran sojojin suka gano raunin harsashin ba.
An yi zargin cewa mutumin ya ci gaba da fafatawa a fagen daga har tsawon mako guda ba tare da wata matsala ba, illa kumburin gefan idonsa.
Sai bayan da likitocin Rasha suka ɗauki hoton wurin sannan suka gano wani babban harsashin bindiga maƙale a ƙwaƙwalwar sojan.
Sun kalli lamarinsa a matsayin abin al’ajabi da ba kasafai yake faruwa ba, kuma a yanzu ana yaba wa mutumin saboda juriyarsa.
Wasu ma suna kira ga sojojin Rasha da su karrama shi da lambar yabo.
Wannan labari da ba a saba gani ba ya tuno da wani labari na yaƙi mai ban mamaki, inda sojan yaƙin basasar Amurka, Jacob Miller, wanda ya rayu tsawon shekara 50 bayan an harbe shi a goshi inda aka yi masa aiki a kwakwalwarsa.
Hotunansa da wani rami da ake gani a goshinsa na ta yaɗuwa a shafukan sada zumunta a yau.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rasha
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye ta bada sanarwan cewa a shirye take da saki fursinonin HKI da Amurka, har ma da gawakin wasu 4, idan HKI ta dawo kan ci gaba da aiwatar da abubuwan da yarjeniyar tsagaita wuta a tsakaninta da HKI.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wani Jami’in kungiyar yana fadar haka a jiya Jumma’a. Ya kuma kara da cewa, wasu daga cikin wadanda suke tsakanin kungiyar da HKI ne ya bata wannan shawarar, sannan ya kara da cewa, sai dai wannan matakin yana da sharudda, kuma sune HKI ta amince ta dawo kan tattaunawa marhala ta biyu don aiwatar da yarjeniyar da aka cimma tsakanin bangarorin biyu.
Taher al-Nounou ya fadawa kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa kan cewa Hamas zata salami Edan Alexander wanda yake dauke da passport na Amurka da kuma wasu 4 wadanda suke dauke da Passport na kasashen biyu wato HKI da kuma Amurka. Amma tare da wannan sharadin.
Sanarwan ta kammala da cewa kungiyar ta fara sabuwar tattaunawa a birnin Doha na kasar Qatar a ranar Talatan da ta gabata sannan tawagar HKI ma tana halattar tattaunawan wand aba kai tsaye ba.