Rundunar sojin Najeriya ta ce za ta fara atisayen tantance gwanintar harbi na shekarar 2025 daga ranar Litinin 17 zuwa 19 ga watan Maris a Barikin Yar Gaba da ke Dutse, Jihar Jigawa.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 26 Armoured Brigade, Laftanar Uzoma Egwu-Ukpai, ya sanyawa hannu aka kuma bai wa gidan rediyon Najeriya a Dutse.

Sanarwar ta bayyana cewa, atisayen tantance gwanintar harbi ana yi ne domin auna ƙwarewar jami’an soji wajen sarrafa makamai da ingancin harbinsu.

Laftanar Uzoma Ukpai ya shawarci al’umma da kada su firgita yayin atisayen idan suka ga sojoji suna kai-komo ko suka ji karar harbi, musamman mutanen da ke zaune a yankin Yargaba.

Haka kuma, Mataimakin Daraktan ya umarci manoma da mafarauta da ke kusa da wurin atisayen da su guji yankunansu na noma da farauta a lokacin atisayen.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Harbi Jigawa Rundunar Soji

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC

Ƙungiyar Ƙwadago a Jihar Sakkwato (NLC), ta musanta iƙirarin da shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta ƙasa (NULGE), Ali Kankara, ya yi cewa gwamnatin jihar ba ta fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 ba.

Shugaban NLC na jihar, Kwamared Aliyu Abdullahi, ya bayyana wa manema labarai a ranar Laraba cewa Gwamnatin Sakkwato ta fara biyan sabon albashin tun a watan Janairu ga dukkanin ma’aikatan jihar, ciki har da na ƙananan hukumomi.

Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi

Ya ce: “Sakkwato ce jiha ta farko da ta fara biyan sabon albashi na dubu 70, kuma ma’aikatan gwamnati da na ƙananan hukumomi na amfana da shi.

“Maganar shugaban NULGE na ƙasa ba gaskiya ba ce.”

Ya ƙara da cewa bai kamata shugaban NULGE ya faɗi irin wannan magana ba tare da ya bincika gaskiyar al’amari ba.

Kwamared Aliyu, ya yaba wa Gwamna Ahmad Aliyu bisa ƙoƙarinsa na biyan ma’aikata haƙƙoƙinsu da kuma dawo da kuɗin tafiyar da ofisoshi, biyan bashin fansho da sauran haƙƙoƙin ma’aikata.

Sai dai wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa ba dukkanin ma’aikatan ƙananan hukumomin jihar ne ke karɓar albashin dubu 70 ba.

Wani ma’aikaci ya ce: “Wasu daga cikinmu da muke karɓar dubu 18 a da, yanzu muna karɓar dubu 30, yayin da waɗanda ke karbar dubu takwas a baya, yanzu gwamnati na biyansu dubu 20.”

Wannan ya nuna cewa duk da gwamnati na ƙoƙarin biyan sabon albashi, har yanzu ba a kai ga kowa ya samu dubu 70 ba a matakin ƙananan hukumomi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • ‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Mamaye Sassan Jihar Borno -Zulum
  • Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji
  • ’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina
  • Sabon Kwamishinan Na Kwara Ya Sha Alwashin Dakile Laifuka
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya
  • Gwamnatin Sakkwato na biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 – NLC
  • Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu
  • Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji
  • NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma