Kamitin Zakka na Masarautar Hadejia ya raba zakkar kayayyakin amfanin gona da na kudi kimanin naira miliyan 63 a gundumar Birniwa dake Jihar Jigawa.

Sakataren kwamitin zakka na masarautar Hadejia, Injiniya Isma’ila Barde, ya bayyana hakan yayin kaddamar da rabon zakka ga mabukata a gundumar Birniwa.

Injiniya Isma’ila Barde ya lissafa abubuwan da aka bayar a matsayin zakka, da suka hada da buhunan Gero 668, da Bahunan Dawa 152 da bahunan shinkafa 8 da rabi da Kuɗi kimanin naira miliyan 17 da dubu ɗari tara da goma sha shida.

A nasa jawabin, Shugaban kwamitin zakka na masarautar Hadejia, Barrista Abdulfatah Abdulwahab wanda babban limamin masarautar Hadejia Ustaz Malam Yusuf Abdurrahman ya wakilta, ya yaba wa al’ummar Birniwa bisa bayar da zakkarsu ga kwamitin masarauta don rabawa mabukata.

Tun da farko, Hakimin Birniwa, Sarkin Arewan Hadejia, Alhaji Abubakar Usman Kariya, ya jinjinawa kwamitin zakka na gundumar bisa zakka da aka tara a gundumar.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

MDD : Kwamitin Sulhu ya yi tir da kisan kiyashin Siriya

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, ya yi Allah wadai da kisan kiyashin da aka yi a baya-bayan nan a yammacin Syria, inda ya yi kira ga hukumomin rikon kwarya a kasar, da su kare “dukkan ‘yan Syria ba tare da nuna bambanci ba,” ba tare da la’akari da kabila, addini ba.

Majalisar ta yi kakkausar suka kan tashe-tashen hankulan da ke faruwa a lardunan Latakia da Tartus tun daga ranar 6 ga Maris, ciki har da kisan kiyashin da aka yi wa fararen hula, musamman a cikin al’ummar Alawite, ‘yan tsirarun da ke da alaka da dangin tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa
  • Ramadan Iftar: Sarkin Kauru Ya Hori Al’umma Su Hada Kai Su Zauna Lafiya da Juna
  • Mahaifiyar Sarkin Gwoza ta rasu
  • Nazarin CGTN: Kasar Sin Na Bayar Da Gudunmuwa Dangane Da Warware Batun Nukiliyar Iran
  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  • MDD : Kwamitin Sulhu ya yi tir da kisan kiyashin Siriya
  • Dan Majlisa Ya Tallafa Wa Al’ummar Mazabarsa Da Kayan Abinci Na Naira Miliyan 45 A Katsina
  • Dangote Da NNPCL Sun Koma Teburin Tattaunawa Kan Cinikin Danyen Mai A Kan Naira
  • Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar da Shari’ar Masarautar Kano Har Sai Kotun Ƙoli Ta Yanke Hukunci