Yadda ango da ’yar uwar amarya suka rasu minti 30 kafin ɗaurin aure a Bauchi
Published: 16th, March 2025 GMT
A lokacin da Abba Musa angon da za a daura wa aure, da wasu mutum huɗu suka kama hanya zuwa kauyen Murno daga garin Boto a Karamar Hukumar Tafawa Balewa a Jihar Bauchi, babu wanda ya yi tunanin cewa shi angon da ’yar uwar amaryarsa, Raihanatu Sulaiman za su rasa ransu mintoci kadan kafin a daurin auren.
Kafin ɗaurin auren ne Abba Musa da Maryam Sulaiman amarya da kuma Rainahatu Sulaiman (’yar uwar amarya) da Misbahu Ahmad (abokin ango) da direban motar sun tafi garin Murno da ke da nisan kilomita 5 daga Boto domin gaisawa da ’yan uwan amaryar kamar yadda aka saba a al’adar Hausawa.
Soja ya shafe mako guda da harsashi a cikin ƙwaƙwalwarsa Nijar ta kori wasu kamfanonin China 3 daga ƙasarA kan hanyarsu ta zuwa garin ne suka yi hatsarin da ya yi sanadiyar mutuwar angon da ’yar uwar amaryar yayin da ita kuma amaryar da sauran mutane uku da ke cikin motar, suka tsallake rijiya da baya da munanan raunuka.
Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa wani mahaukaci ne ya yi sanadiyyar hatsarin a yayin da yake ƙoƙarin tsallaka titi.
An ce direban ya yi iya ƙoƙarinsa don kauce wa mahaukacin, amma motar ta ƙwace masa ta yi sama, sannan ta faɗo ƙasa, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane biyu tare da jikkata sauran uku da ke cikinta.
Wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, angon ya samu mummunan bugu a kansa, nan take ya mutu, ’yar uwar amaryar kuma ta rasu ne a asibiti a yayin da ake yi mata magani.
Ita kuma amaryar ta samu karaya a ƙafarta da kuma rauni a hannunta da kafadarta, yayin da direba da abokin angon suka samu raunuka a hannu da ƙafafu.
Mahalarta ɗaurin aure sun shiga alhiniDaruruwan mahalarta ɗaurin auren daga nesa da kusa da suka yi dandazo a garin Boto domin bikin sun faɗa cikin dimuwa da jimami bayan faruwar lamarin, mintoci 30 kafin daurin auren.
Wani ganau ya ce hatsarin ya faru ne a ƙarshen makon shekaranjiya da misalin ƙarfe 1:35 na rana.
Wani ɗan uwan angon mai suna Alhaji Saminu Abubakar Boto, ya bayyana yanayin da al’umma ke ciki a matsayin abin baƙin ciki matuƙa.
Ya ce, “Asara ce da ba za a iya misalta ba. Al’umma gaba ɗaya suna alhinin rasuwar sirikina da kuma kanwata Raihanatu.
“Iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su sun fada cikin ruɗani, inda ’yan uwa da abokai ke kokawa kan kan wannan babban rashi, ba zato ba tsammani.”
Alhaji Boto ya bayyana cewa gidan dangin amaryar da ke cikin hidimar ɗaurin auren, ya koma wurin zaman makoki da zubar hawaye bayan afkuwar lamarin.
An garzaya da mahaifin ango asibitiBayan samun labarin faruwar lamarin, nan take mahaifin angon ya yanke jiki ya faɗi aka garzaya da shi asibiti, inda likita ya bayyana cewa jininsa ya hau 260 sama da 220.
Ita ma mahaifiyar angon ta faɗi lokacin da aka ba ta labarin rasuwar ɗanta.
Alhaji Boto ya ce, “Har zuwa lokacin da nake magana da ke, ’yar uwata, amaryar ta kasance cikin kaduwa da tashin hankali.
“Ban san yadda zan kwatanta lamarin ba. Lallai abin tausayi ne. Sama da mutane 4,00 ne suka shiga gidanmu domin jajantawa bisa wannan bala’in da ya faru,” inji shi.
Ya bayyana Marigayi Musa a matsayin “Saurayi mutumin kirki mai mutunci da kamun kai wanda ya yi fatan kafa iyalinsa tare da ‘yar uwata, Maryam Suleiman, amma da yake Allah Ya sa hakan ba zai yiwu ba saboda rasuwarsa.
Ganawar ƙarshe“Angon na zaune ne a garin Buruku da ke Jihar Filato. Ya zo Boto daga Jos ne domin ɗaurin aurensa, sai muka yi ta barkwanci tare da abokai, ‘yan mintoci kadan kafin su wuce kauyen Murno.
“Cikin zolaya yake ce min in je in sa babbar-riga. Na ce masa idan na saka, mutane za su dauka ni ne ango. Muka yi dariya. Da gama hirarmu suka tafi Murno domin gaishe da ”yan uwa. Sai dai kash, maganata ta ƙarshe da shi ke nan.
“Lokacin da za a je ɗaura auren ni ne na ɗauko babana da abokansa a motata zuwa gidan amaryar, bayan mun isa aka aiko ana nema na a babban asibitin kusa da gidan amaryar. Da na je aka shaida min cewa motar da ta kai ango ƙauyen Murno ta yi hatsari.
“Da isowata na tarar da gawarsa a shimfide a kan gadon da yankan karfe ko gilashi a kansa, a yayin da amaryar, Maryam, Raihanatu, Misbahu da direban motar ke karɓar magani wurin masu ba da agajin gaggawa. Bayan mintoci kaɗan kuma aka tabbatar da mutuwar Raihanatu.
Yankan ƙauna“Za a riƙa tunawa da Raihanatu a matsayin ‘yar uwa wacce ta taka muhimmiyar rawa wajen tsara bikin auren da ba a cika yin irinsa ba.
“Ta shiga mota ita da ango zuwa Murno domin ita da amarya ne kawai suka san gidan danginmu na ƙauye; kuma a al’adance, amarya ba za ta bude fuskarta don jagorantar direba ba.
“Wannan mummunan lamari ya jefa al’umma cikin ruɗani, inda yawancin mazauna garin suke bayyana shi a matsayin daya daga cikin ranaku mafi bakin ciki a cikin ‘yan kwanakin nan.
“Ba mu taɓa ganin irin wannan abin takaici irin haka ba a cikin wannan gari. Za a daɗe iyalai da abin ya shafa ba su manta wannan lamarin ba,” in ji shi.
Wakilin Aminiya ya ta tattaro bayanan cewa an yi jana’izar duk mamatan kamar yadda addinin Musulunci ya tanada jim kaɗan bayan faruwar hatsarin, yayin da amaryar ke cikin mawuyacin hali sakamakon mummunan raunuka da kuma rashin masoyi da ‘yar uwarta a ranar da ya kama ta tafi kowace farin ciki a wajenta
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amarya Hatsari Jihar Bauchi Jihar Filato Mutuwa ɗaurin auren
এছাড়াও পড়ুন:
Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
Wata mata mai suna Jennifer Castro ta shigar da ƙarar kamfanin jiragen sama na GOL da wata fasinja a kotu bisa wani faifan bidiyo aka wallafa da yake nuna matar ta ki barin kujerarta da ke kusa da taga saboda wani yaro da yake kuka.
Matar ’yar ƙasar Brazil da ta ƙi barin kujerar kusa da taga saboda wani yaro mai kuka ta shigar da ƙara a kotu.
Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen FilatoJennifer Castro, mai shekara 29 na daukar matakin shari’a a kan kamfanin jiragin sama na GOl da kuma fasinjar da ta ɗauki bidiyonta a lokacin da lamarin ya faru.
Lamarin wanda aka yi ta yadawa ta intanet, ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a.
A cewar jaridar The New York Post, Castro na tuhumar kamfanin jirgin da kuma matar da ya nadi musayar takaddamar da suka yi, inda ta nemi diyya kan halin kunci da barnar da lamarin ya haifar mata.
Ta bayyana cewa, matakin da ta ɗauka na shigar da ƙarar shi ne don hana afkuwar irin wannan abin kunya ga jama’a a nan gaba.
Al’amarin ya ja hankalin jama’a saboda yada lamarin a kafafen sada zumunta.
Da take bayani a kan shari’ar, Castro ta ki bayyana adadin diyyar da take nema.
Ta ce, tana son hana irin wannan tozarta jama’a da abin da ta kira fallasa ba tare da izini ba a nan gaba.
Hakan na zuwa ne bayan da aka bayar da rahoton cewa, a watan da ya gabata ta fara “tunanin” daukar matakin shari’a.
Castro ta bayyana cewa, “tun bayan faruwar wannan lamarin, rayuwata ta shiga wani yanayi da ban taba tunanin sa ba.”
“Abin da ya kamata ya kasance kawai jirgin zirgazirgar na yau da kullun ya sauya zuwa wani abun kunya, yana fallasa ni da rashin adalci da haifar da sakamakon da ya shafi rayuwata ta sirri da ta sana’a.
Ni ce ake so na yanke hukunci a kan takaddama da hasashen mutanen da ba su ma san cikakken labarin ba.”
Castro ta ce lamarin ya fara ne a lokacin da take hawa jirgi, sai ta hangi wani yaro a zaune a lambar kujerar da ya kamata ta zauna.
Tunda ta riga ta zabi wurin zama na kusa da taga, Castro ta yi tsammanin yaron zai koma wani wurin zaman na daban.
“Na jira shi yadda ya kamata, amma ya kwantar da kansa a wata kujerar, sannan sai na zauna a kujerata ,” in ji ta.
Lamarin ya ta’azzara lokacin da wata ta fara daukar bidiyon Castro ba tare da izininta ba.