Kungiyoyin Falasdinawa Suna Cigaba Da Yin Allawadai Da Hare-haren Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
Published: 16th, March 2025 GMT
Kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Hamas ta yi Allawadai da Hare-haren Amurka da Birtaniya akan kasar Yemen
Kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Hamas ta fitar da bayani na yin tir da hare-haren da jiragen yakin Amurka da Birtaniya su ka kai wa Birnin San’aa a jiya Asabar da dare.
Ita ma kungiyar Jihadul-Islami ta fitar da bayani na yin Allawadai da Amurka saboda harin da ta kai wa Yemen din, tana mai bayyana abinda ta aikata da cewa abin kunya ne da nuna goyon bayan ga laifukan da HKI take aikatawa akan al’ummar wannan yankin.
Kungiyar Jiahdul-Islami ta kuma yi jinjina ga kasar Yemen saboda yadda su ka tabbatar da jarunta ta asali irin ta Larabawa da musulmi wajen nuna goyon bayan mutanen Gaza da al’ummar Falasdinu.
Kwamitin al’umma na goyon bayan gwgawarmayar al’ummar Falasdinu ya bayyana harin na Amurka da Birtaniya akan Yemen da cewa, nuna goyon bayan ne karara ga HKI.
Bayanin ya kuma ce; Maharan ba za su karya kashin bayan al’ummar Yemen ba da suke tsayin daka wajen taya Falasdinawa fada da kalubalantar killace mutanen Gaza da HKI ta yi, bisa goyon bayan Amurka.
Ita kuma kungiyar “Harkatul-Mujahidin” ta yi kira ne ga rayayyun al’ummu da ‘yan gwgawarmaya da su hada karfi da karfe domin fuskantar wuce gona da irin ‘yan sahayoniya da Amurka, tare da kara da cewa; Babu abinda zai takawa masu daga hancin da girman kai, birki,sai karfi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Amurka da Birtaniya na goyon bayan
এছাড়াও পড়ুন:
Mayakan “Jubhatun-Nusrah’ Na Kasar Syria Sun Kai Hari Akan Iyakar Kasar Leabnon
A jiya Lahadi ne dai kungiyar ta ‘yan ta’adda ta kai hare-hare akan iyakar Lebanon ta yankin Hermul
Ma’aikatar tsaron Syria ta fitar da wata sanarwa da a ciki ta riya cewa; harin nata martani akan wani hari da aka kai a can cikin kasar wanda ta jinginawa HIzbullah, da kuma ya yi sanadiyyar mutumar jami’an tsaro uku.
Kungiyar ta Tahrirush-sham ta yi amfani da makamai rokoki da atalare wajen kai hari daga kan iyaka.
Tuni dai kungiyar Hizbullah ta fitar da wata sanarwa da a ciki ta karyata zargin na kungiyar Tahrirus-sham.
Ofishin da yake kula da watsa labaru na Hizbullah ya bayyana cewa; Babu gaskiya a cikin labaran da ake watsawa na cewa Hizbullah tana da hannu a cikin abinda yake faruwa akan iyakar Lebanon da Syria.”
Sanarwar ta kuma kara da cewa; Muna sake jaddada cewa ba mu da alaka da duk wani abu da yake faruwa a cikin kasar Syria.
Wata kafa ta watsa labarai ta kasar Lebanon ta ce; kungiyar Agaji ta “Red Cross” ta mika gawawwakin wasu mayakan kasar Syria su uku da aka kashe, ba tare da cikakken bayanin yadda aka kashe sub a.
Haka nan kuma majiyar ta bayyana cewa; an harba makamai masu linzami a cikin garin al-kasar da yake akan iyaka.
Ma’aikatar tsaron Syria ta sanar da kai hari da manyan bindigogi akan wasu garuruwa Lebanon da suke a kan iyaka.