Da safiyar yau Lahadi, sojojin Amurka da Birtaniya sun ci gaba da kai wa kasar Yemen hare-hare, inda a bayan nan su kai wasu jerin hare-hare guda uku.

Yankunan da hare-haren na Amurka da Birtaniya su ka shafa a cikin Yemen sun hada “ali Sabba”, dake gundumar Sahhar, da hakan ya yi sanadiyyar kashe daruruwan dabbobi.

Haka nan kuma sojojin na Amurka sun kai wasu hare-haren a gabashin Majzar, dake gundunar “Ma’arib”.

Tun da marecen Asabar ne dai sojojin na Amurka su ka shelanta kai wa Yemen hare-hare a biranen San’aa,Sa’adah, da Zammar.

A birnin Sa’adah, kananan yara 4 sun yi shahada sai kuma wata mace, yayin da wasu mutane fiye da 10 su ka jikkata.

Wasu yankunan da hare-haren na Amurka su ka shafa sun hada da  yankunan Mikra da kuraishiyya a gundumar Baidha’a.

A yankin Jarf, dake birnin San’aa mutane 9 ne su ka yi shahada.

Tashar talabijin din ‘almasirah’ ta kasar Yemen ta bayar da labarin dake cewa jumillar wadanda su ka yi shahada sun kai 24, 14 daga cikinsu a birnin Sanaa,sai kuma  10 a Sa’adah. Haka nan wani adadin da ya kai  23 sun jikkata.

Kungiyar Ansarullah ta Yemen ta jaddada ci gaba  da kai wa jiragen ruwan HKI hare-hare a ruwan “Red sea” har zuwa lokacind a za a kawo karshen hana shigar da kayan agaji ga mutanen Gaza masu azumin Ramadan.

Daga marecen jiya Asabar zuwa tsakar dare, sau 30 Amurka da Birntaniyan su ka kai wa Yemen hare-hare.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci 

Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin da wani ɗan majalisar Amurka, Chris Smith, ya yi cewa ana tauye wa Kiristoci ’yancin addini a Najeriya.

Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa matsalolin tsaro da ake fuskanta ba su da alaƙa da addini, domin hare-haren ’yan ta’adda na shafar dukkanin Musulmi da Kiristoci.

Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — Obasanjo Wadda ke damfara da sunan matar gwamnan Katsina ta shiga hannu

Tuggar ya ce hare-haren da ake kai wa a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma ba sa ware mabiyan wani addini.

Gwamnatin Tarayya ta nuna damuwa kan yadda ake yaɗa rahotannin da ba su dace ba, waɗanda ka iya haddasa rarrabuwar kawuna a ƙasar.

Rahoton wata ƙungiya mai suna Open Doors ya ce kashi 89 na Kiristocin da ake kashewa a duniya na faruwa ne a Najeriya.

Sai dai ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta musanta hakan, inda ta ce Musulmi ne ma aka fi kashewa a tashe-tashen hankulan da ake fama da su.

Tun a zamanin mulkin Trump, Amurka ta saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargin suna tauye ’yancin addinin Kiristoci.

Sai dai Gwamnatin Tarayya ta ce wannan batu ba shi da tushe balle makama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Adadin Shahidan Falasdinawa A Gaza Ya Karu Da 14 A Jiya Lahadi Saboda Hare-Haren Sojojin HKI
  • Kungiyar Ansarullah Ta Ce Keta Hurumin Kasar Da Amurka Ta Yi Zai Gamu Da Maida Martani
  • Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina
  • Kungiyoyin Falasdinawa Suna  Cigaba Da Yin Allawadai Da Hare-haren Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
  • Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina 
  •  Sojojin Kungiyar  “SADC” Sun Janye Daga DRC
  • Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci 
  • HKI Tana Cigaba Da Keta Tsagaita Wutar Yaki A Lebanon