Ma’aikatar Harkokin Wajen JMI Ta Yi Allawadai Da Kungiyar G7 Wacce Ta Zargin Kasar Da Abubuwa Da Dama
Published: 16th, March 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baka’e ya tir da kungiyar kasashe 7 masu karfin tattalin arziki a duniya,wato G7.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Baghaee yana fadar haka a jiya Asabar, ya kuma yi All..wadai da zarge zagren kungiyar wadanda suka hada da zargin Iran da kokarin mallakar makamin Nukliya, da hadsa fitina a kudancin Asia.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran yace dukkan wadannan zarge-zarge basa da toshe.
Sannan ya zargi kasashen kungiyar na G7 da goyon bayan HKI a kissan kiyashin da ta aikata a Gaza.
Kafin haka dai kasashen kungiyar ta G7 sun kammala taronsu a kasar Canada a ranar jumma’ar da ta gabata inda suka, suka fidda bayanin bayan taro wanda yake zargin Iran da taimakawa kasar Rasha da makaman da take yakar kasar Ukraine, da neman mallakar makaman nukliya da kuma rikita kasashen yankin Asia.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Yaba Da Yarjeniyar Zaman Lafiya Da Aka Cimma Tsakanin Kasashen Armenia Da Azerbaijan
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeskiyan ya ba da sanya hannu a kan takardun yarjeniyar samar da zaman lafiya wanda kasashen Armenia da Azerbaijan suka yi. Ya kuma taya mutanen kasashen murmurnar wannan nasara.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban yana taya kasashen biyu murna a jiya lahadi, ya kuma kara da cewa, Iran a ko yauce tana fatan zaman lafiya a kasashe makobata da kasar sabuda dalilai da dama daga ciki Iran tana amfani da kasashe makobta don kyautata yanayin tattalin arziki a tsakanin kasashen biyu.
Firai ministan kasar Armenia Nikol Pashjinyan a zantawarsa ta wayar tarko da shugaban kasar Iran ya ce: Gwamnatinsa zata yi kokarin ganin an aiwatar da yarjeniyar daki daki kamar yadda aka tsara ta.
Kasashen biyu dai sun tabka manya-manyan yake yake a tsakaninsu, wadanda suka hada na shekara 1992 kan yankin Nagornu Karabal, sai kuma na shekara ta 2023 inda aka kashe mutane kimani 30,000 a tsakaninsu.
A shekara ta 2023 Azerbaijan ta kwace iko da yankin Nagorno Karabak wanda a dokokin kasa da kasa yankin Azerbaijan ne amma yan kabilar azari basu fi kasha 20% a yankin ba a yayin da sauran kuma Armeniyawa na. Kasashen biyu sun sami yanci ne a shekara 1991 bayan rushewar tarayyar Soviet.