HausaTv:
2025-03-16@14:10:29 GMT

Iran Tace: Amurka Bata Da Hakkin Tsara Mana Yadda Zamu Tafiyar Da Kasar Mu

Published: 16th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran y ace gwamnatin kasar Amurka bata da hakkin tsarawa kasar Iran yadda zata gudanar da manufofinta harkokin waje, wannan ya wuce tun bayana nasarar juyin juya hali musulunci a kasar a shekara ta 1979.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a shafinsa na X.

Aragchi yana maida martani ne ga shugaban kasar Amurka Donal Trump wanda ya tuta sojojinsa suka kai hare-hare kan kasar Yemen a jiya Asabar, don kada su hana jiragen ruwan HKI wucewa daga tekun Red Sea. Kuma ya ce: Ya gargadi Iran ta dakatar da tallafin da take bawa kungiyar Ansarullah. Don itace da alhakin duk abinda kungiyar take yi.

Ministan ya kara da cewa, ya maida martani da cewa: Amurka ce da alhakin marawa ayyukan ta’addancin da HKI take aikatawa a duniya, kuma gwamnatin shugaban Biden kadai ta kashe dalar Amurka biliyon 23 don kissan Falasdinawa kimani 60000 a Gaza. Don haka yana kira ga Amurka ta dakatar da tallafin da take bawa HKI wacce mafi yawan kasashen duniya ta dauketa a matsayin yar ta’adda.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Tehran a shirye take ta shiga tattaunawa da kasashen Turai bisa mutunta juna.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Araghchi da Ministan Harkokin Wajen Netherlands Caspar Veldkamp sun tattauna hanyoyin inganta alakar juna da sabbin abubuwa dake faruwa a yankin da na kasa da kasa.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya nanata tsarin kasar na kulla kyakkyawar alaka ta diflomasiyya da kasashen.

Iran da kasashen Turai dai na tattaunawar ba-zata kai a kai tun shekara ta 2021, shekaru uku bayan da Amurka ta fice daga yarjejeniyar nukiliyar iran – tare da maido da takunkumin da Washington ta kakaba wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

bangarorin kasashen Turai da suka shiga yarjejeniyar nukiliya – Birtaniya, Faransa da Jamus – sun kasa cika alkawarin da suka dauka na dawo da Washington cikin yarjejeniyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kofar JMI A Bude Take Don Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi
  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • Amurka Ta Ce Bata Bukatar Jakadan Kasar Afirka Ta Kudu A Kasar, Bayan Da Ya Aibata Shugaba Trump
  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  • Yadda Nijeriya Ta Zarce Yawan Man Da OPEC Ta Ware Mata – Bincike
  • Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta
  • Duniyarmu A Yau: Martani Jagora Ga Trump kan Shirin Nukliyar Kasar Iran