Mai Martaba Sarkin Kauru dake Jihar Kaduna Alhaji Zakari Ya’u Usman ya bukaci samun hadin kai da aiki tare kana da hakuri da juna tare da ɗaukar banbance banbance dake tsakanin al’umma a matsayin wata baiwa.

Alhaji Zakari Ya’u II yayi wannan horonne lokacin da aka taru a fadarsa dake Kauru domin shan ruwan azumin Ramadan.

Mai martaban ya bayyanawa wadanda suka taru domin wannan aikin lada na shekara shekara cewa, akwai bukatar yafiya da ‘yan uwantaka a wannan lokaci na Ramadan tare da godiya ga Allah da ya sake nuna mana wannan watan mai albarka.

Alhaji Zakaria Ya’u Usman yace akwai bukatar sadaukarwa da mika wuya ga Allah da kankantar da kai tare da fahimtar cewa wannan banbanci da ke tsakanin al’umma wata baiwa ce daga huwallazi tare da kira ga jama’a su nuna godiya ga Allah da wannan baiwar.

Yace Allah baya kuskure, saboda haka mu dauki wannan banbancin dake tsakanin mu a matsayi wata hanya ta aiki tare da nuna karfin mu na zama al’umma daya.

Sarkin Kauru ya godewa gwamnan jihar Kaduna Uba Sani saboda samarda zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kaduna tare da gamsuwa da yunkurin karamar hukumar Kauru da jami’an tsaron wajen samar da kwanciyar hankali musamman kalubalen tsaron da wasu miyagun mutane suke haddasa wa a yankin.

Ganin yadda bukukuwan sallah ke karatowa, mai martaba ya hori talakawansa su kasance masu riko da kyawawan dabi’u da yafewa juna tare da tunatar da su cewa watan Ramadan ba wai ana magana akan azumi ne kadai ba, akwai bukatar ganin sa a ayukkan mu na yau da kullum.

Haka Kuma, sakataren masarautar Muhammad Sani Suleiman (Dan Buran Kauru) ya nanata kudurin masarautar na samarda zaman lafiya da hadin kai tsakanin al’ummar yankin.

Radio Nijeriya Kaduna ya bada labarin cewa an kammala wannan bikin shan ruwa na masarautar Kauru da gudanar da addu’o’in samun zaman lafiya da ci gaban al’ummar yankin a daidai lokacin da ake shirin bukukuwan sallah.

Yusuf Zubairu Kauru 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan Iftar Sarkin Kauru Zauna Lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3

’Yan bindiga sun kai hari tare da tarwatsa mazauna ƙauyuka biyar da ke Karamar Hukumar Kachia a Jihar Kaduna.

Ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Unguwan Tauka, Unguwan Lalle, Sonudazuwa, Tsauni Dodo, da Dandauka.

Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — Obasanjo

Wani jagoran al’umma ya tabbatar da faruwar harin, inda ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun kuma kai farmaki sansanin Fulani da ke Kubuwo, inda suka sace matasan makiyaya uku.

Sun kai harin ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 6 na yamma.

Shaidu sun bayyana cewa ’yan bindigar sun isa ƙauyukan suna harbe-harbe, lamarin da ya tilasta wa mazauna ƙauyukan tserewa.

“’Yan bindigar sun shigo suna harbi ta ko ina. Mutane suka riƙa gudu don tsira da rayukansu,” in ji wani jagora.

“Sannan sun sace matasa uku a sansanin Fulani, suka tafi da su cikin daji.”

Wani jami’in tsaro ya bayyana cewa ’yan bindigar sun tserewa wani farmaki da sojoji suka kai musu a dajin Kurutu-Azara, wanda ke iyaka da Ƙaramar Hukumar Kagarko.

Ya ce a kan hanyarsu ta tserewa ne, suka farmaki ƙauyukan da ke hanyarsu.

A yayin harin, ’yan bindigar sun ƙone mota da babur a Unguwan Tauka.

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa, “An ƙone wa wani mutum mota sabuwa da ya sayo a Kaduna. Yana kan hanyar shigowa garin ne sai ya hango ’yan bindigar.

“Nan take ya fice daga motar ya tsere, suna ganin motar suma cinna mata wuta suka ƙone motar da wani babur.”

Wani ɗan banga daga cikin ƙauyukan da aka kai wa harin ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na ci gaba da bin sahun ’yan bindigar.

Rundunar ’yan sandan yankin ta tabbatar da harin, amma ta ce za a tuntuɓi hedikwatar ’yan sandan m Kaduna don ƙarin bayani.

Sai dai kakakin rundunar, ASP Hassan Mansur, bai samu damar yin tsokaci kan harin ba lokacin da aka nemi jin ta bakinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahaifiyar Sarkin Gwoza ta rasu
  • Masarautar Hadejia Ta Raba Zakka Ta Kimanin Naira Miliyan 63 Ga Mabukata
  • Harin da Isra’ila ta kai ya kashe Falasdinawa 9 a arewacin Gaza
  • Majalisa Ta Bukaci CBN Ya Gaggauta Dakatar Da Karin Caji A ATM
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • Iran Ta Yi Tir Da HKI Da Kokarin Wanke Kanta Tare Da Rabawa Addinin Musulunci Ta’addanci
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]
  • ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3
  • Matsalar Tsaro: Shugaban Ƙaramar Hukuma ya tabbatar da haɗa kai da Sarakuna