Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar ‘Yan Majalisu
Published: 16th, March 2025 GMT
“…The composition and functioning of the legislatibe council, howeber, pointed to the fact that, it was nothing more than a mere rubber-stamping institution…”.
(Fagge & Alabi, 2007: 5b).
Wadancan kalamai na sama cikin harshen Turanci, na yin nuni ne da cewa, “yan majalisun Nijeriya a wancan lokaci da Turawan Birtaniya ke mulkarmu, ba su kasance komai ba, face “yan-abi-yarima ne cikin harkokin zaman majalisar.
Batun rashin iko, ko karancinsa, shi ne babban abinda ya mamaye harkokin “yan majalisun na kasa gabanin Nijeriya ta kai ga samun “yancin-kai. Sai dai, a kan samu wasu “yan canje-canje ne daga lokaci zuwa lokaci, sakamakon mabanbantan kundin tsarin mulkin da Turawan suka gabatar mana da su gabanin kai wa ga samun yancin-kai. Tulin labaran “yan majalisun na da auki ainun, kawai za mu yi kokarin matsawa gaba ne cikin hanzari, don kai wa ga yadda lamuran majalisar ke wakana a yau, wanda shi ne babban abinda muke son yin doguwar tattaunawa akai sannu a hankali.
“Yan Majalisunmu A Shekarar 1900
Ya tabbata, bayan samun “yancin-kai a wannan Kasa (cikin Shekarar 19b0), “yan majalisun namu, sun kai ga fara samun “yancin gudanar da aiyukansu, sama da irin yadda suka kasance a baya. Tsarin mulki irin na shugaban kasa daban, da shugaban gwamnati (tsarin mulkin firaminista) daban, aka fara dabbakawa a wannan kasa bayan samun mulkin kai. A karkashin tsarin mulkin, za a ga irin aikace-aikacen da wadannan ‘yan majalisun namu na lokacin suka gudanar, kafin juyin mulkin Soja na farko da aka fara yi a kasar, cikin Shekarar 19bb, Shekaru shida (b) kacal, bayan samun yancin-kai. Ke nan, irin ayyukan da suka gudanar cikin majalisar, zai zamto ne a tsakanin Shekarar 1900 da Shekarar 1900.
Ga wasu daga irin ayyukan da bangaren “yan majalisun suka gudanar kamar haka;
i- Kafa Gwamnati: “yan majalisun ne suka taka rawa wajen zabar firaminista Abubakar Tafawa Balewa a matsayin shugaban gwamnati, tare da yunkurin fasalta tsarin gwamnatin dimukradiyya.
ii- Ci gaban bangaren dokoki: “yan majalisun, sun samar da dokoki kyawawa, musamman wadanda suka shafi ci gaban tattalin arzikin kasa, ilimi tare da samun cikakken ikon gudanarwa a cikin lardunan kasar da ake da su.
iii- Kyautata Wakilci A Gwamnatin Hadaka Da Na Larduna: tsarin, ya ba da dama ga jagororin gwamnati (firimiyoyi) na lardunan arewa da yamma da na gabashin kasar, na su shigo cikin lamuran gudanar gwamnati dumu-dumu, don a dama da Canji
iv- Canjin Mirginawar Tsarin Mulki Na Kasa: “yan majalisun, sun taka rawa muhimmiya, wajen dawowar tsarin mulkin dake nuna lamuran Kasar, na gudana karkashin ikon Sarauniyar Birtaniya ne, zuwa ga wata jamhuriya mai zaman kanta cikin Shekarar 19b3, wadda ikonta ya sabbawa Dr Nnamdi Azikiwe zama shugaban kasar Nijeriya na farko.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yan majalisun na tsarin mulkin
এছাড়াও পড়ুন:
Hasashen Samun Ruwan Sama A 2025: Shawarwarin Da Kwararru Suka Bai Wa Manoma
Saboda haka ne, hukumar ta shawarci manoman da ke da ra’ayin noma a kakar noman ta bana da su tabbatar sun tuntube ta, ko kuma tuntubar sauran hukumomin da ke hasashen yanayi, domin sanin lokacin da ya ya fi dacewa su yi shuka.
Hukumar ta yi hasashen cewa, jihohin Zamfara, Katsina, Kano, Kaduna, Jigawa, Filato, Bauchi, Borno, Yobe, Adamawa, Taraba, Neja, Kwara, Kogi, Abuja, Ekiti da kuma Ondo, za su fuskanci daukewar ruwan sama da wuri, inda aka kwatanta da na dogon zango da aka samu a daminar bara.
Haka zalika, hukumar ta yi hasashen cewa; za a samu jinkirin ruwan sama a wasu sasssan jihohin Kaduna, Nasarawa, Benuwe, Legas, Kwara, Taraba, Oyo, Ogun, Kuros Riba, Delta, Akwa Ibom, Ebonyi, Anambra da kuma Enugu.
A cewar Hukumar, mai yiwuwa kakar daminar ta bana ta kasance gajera a wasu sassan Jihohin Borno da Yobe, sabanin yadda aka saba gani.
Hukumar ta yi hasashen cewa, mai yiwuwa kakar daminar ta bana, ta yi tsawo a Jihohin Legas da Nasarawa, sabanin yadda aka saba samu.
Hukumar ta yi hasashen cewa, daga watan Mayu zuwa na Yuni, za a samu ruwan sama kamar da baakin kwarya, wanda kuma mai yiwuwa, a samu afkuwar ambaliyar ruwa a wasu biranen da ke kusa da rafuka a kasar.
Kazalika, daga watan Afirilu zuwa na Mayu, yankunan Saki, Iseyin, Ogbomoso, Atisbo, Orelope, Itesiwaju, Olorunsgo, Kajola, Iwajowa da kuma Oro Ire da ke cikin Jihar Oyo, an yi hasashen samun karancin ruwan sama, wanda zai iya kai wa har tsawon kwana 15, bayan saukar ruwan saman.
Bugu da kari, Hukumar ta yi hasashen cewa; a wasu jihohin da ke Arewacin kasar nan, daga watan Yuni zuwa Yuli har zuwa watan Agustan 2025, za a samu karancin ruwan sama, wanda zai kai har tsawon kwana 21, inda kuma a Jihohin Ekiti, Osun, Ondo, Ogun, Edo, Ebonyi, Anambra, Imo, Abia, Kuros Riba, Delta, Bayelsa da kuma Akwa Ibom, za a samu ruwan sama na tsaka-tsaki da zai kai kwana 15.
Daga tsakanin kwana 27 zuwa 40, za su shige ba tare da wani batun hasashe samun sauyin yanayi ba, haka za a fuskanci rani kadan a yankin Kudu Maso Gabas daga ranar 22 na 2025.
Saboda haka ne, kwararru a fannin aikin noma suka shawarci manoman kasar nan, musamman wadanda ke jihohin da ke tsakiyar kasar, da su tabbar da sun yi shuka da Irin da ke jurewa kowanne irin yanayi, musamman domin kauce wa fuskantar matsalar rashin samun saukar ruwan sama a kan lokaci a kakar noman ta 2025.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp