Aminiya:
2025-04-16@21:51:50 GMT

HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalma

Published: 16th, March 2025 GMT

Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta NDLEA sun cafke wasu mutane da hodar iblis da suka ɓoye a cikin carbi da kuma takalma.

A cewar hukumar, an cafke ababen zargin ne yayin da suke ƙoƙarin safarar hodar iblis ɗin zuwa ƙasa mai tsarki.

Femi Babafemi, darektan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na NDLEA ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa tare da hotunan hodar iblis ɗin da aka kama.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hodar iblis hodar iblis

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar

Rahotanni daga Nijar na cewa dakarun tsaron ƙasar sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kama ‘yan bindiga 12 a yankunan Dosso da Diffa na ƙasar.

Kafar watsa labarai ta ActuNiger ta ruwaito cewa a Boumba da ke yankin Dosso ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu bayan dakarun da ke sintiri sun yi arangama da ‘yan ta’addan da suka je daga yankin Falmey.

Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina

Kazalika ranar Alhamis ne dakarun tsaron ƙasar suka yi nasarar kama ‘yan bindiga 12 a ƙauyen Jagada da ke yankin Diffa.

TRT ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a ƙauyen kuma suka fara yi wa mutane ƙwace.

Ana cikin haka ne mutane suka kira dakarun tsaron da ke ƙauyen Kablewa mai maƙwabtaka kuma dakarun suka kai wa mutanen ƙauyen Jagada ɗauki, inda suka yi nasarar kama 12 daga cikin maharan tare da ƙwace bindigogi biyu ƙirar AK47.

Domin ƙarfafa tsaro a ƙauyen da kuma hana ramuwar gayya daga ‘yan bindigar, an samar da ‘yan sintiri na dindindin da suke sun yawo a cikin ƙauyen.

An garzaya da mutane biyun da suka ji rauni a harin asibitin Kablewa inda a yanzu suke samun kulawa.

Har wa yau, dakarun Nijar sun yi nasarar kama mutum biyu masu yi wa ISWAP safarar kayayyaki a yankin Diffa.

Waɗannan nasarorin na zuwa a lokacin da sojin ƙasar ke ƙoƙarin katse hare-haren ‘yan ta’adda da ƙasar ke fama da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC Ta Kama Wasu Mutane 40 Da Ake Zargi Da Yin Damfara Ta Intanet A Neja
  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
  • Mizanin Hada-hadar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 5.4% A Rubu’in Farko Na Bana
  • HOTUNA: Zulum ya karɓi baƙuncin Majalisar Sarakunan Arewa a Borno
  • Isra’ila ta kashe Palasdinawa 17 ta jikkata 69 a awa 24 a Gaza
  • Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
  • Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe