Cikar FRCN Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Jihohin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon
Published: 16th, March 2025 GMT
An yi kira ga gwamnatocin jihohin Arewacin Najeriya da su tabbatar da dorewar tashar Rediyon Nigeria (FRCN) Kaduna a matsayin abim tunawa da marigayi Firimiyan tsohuwar jihar Arewa, Alhaji Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto, ya bari.
Masu sauraron tashar sun yi wannan kira a cikin bayanai daban-daban yayin da suke tsokaci kan bikin cika shekaru 63 da kafuwar gidan rediyon a watan Maris na shekarar 1962.
Sun bayyana godiyarsu ga rawar da FRCN Kaduna ya taka tsawon shekaru duk da kalubalen aiki, wanda suka bukaci mahukunta su magance.
A sakon taya murna daban da suka aiko, Sanata Salisu Musa Matori, da Alhaji Umar Dembo, da Alhaji Umar Iya Gulak, da Alhaji Garba Baba da Alhaji Muhammad Damak Abubakar, sun jinjinawa gidan rediyon bisa bajintar da ya nuna, inda suka jaddada bukatar Gwamnatin Tarayya ta cika alkawuran da ta dauka na farfado da tashar.
Jami’in hulɗa da jama’a na Kungiyar Manoma ta Najeriya, Alhaji Muhammad Magaji, ya nuna matukar jin dadinsa kan yadda tashar ke tallafawa harkokin noma, zaman lafiya, hadin kai, da cigaban kasa. Yana mai kira da a cigaba da wannan yunkuri don cimma manufofin da aka sanya a gaba.
Daga Suleiman Kaura.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Shekaru 63
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina
Dakarun Sojin Saman Najeriya (NAF), sun kashe manyan shugabannin ’yan bindiga guda biyu, Gero (Alhaji) da Alhaji Riga, tare da wasu mayaƙansu sama da 20 a wani hari ta sama da suka kai a Jihar Katsina.
Harin ya faru ne a ranar Laraba, 13 ga watan Maris, a dajin da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.
Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci Kotun ɗaukaka ƙara ba ta soke naɗin Sanusi II ba — Gwamnatin KanoRundunar Operation Fansan Yamma ta NAF ce ta ƙaddamar da harin bayan samun sahihan bayanai kan maɓoyar maharan.
A cewar Mataimakin Kakakin NAF, Kyaftin Kabiru Ali, ya ce dakarun sun lalata sansanin maharan.
“An kashe ƙarin ‘yan ta’adda a tsaunukan da ke kusa, kuma har yanzu ana ci gaba da binciken irin ɓarnar da aka yi musu,” in ji shi.
Gero da Riga sun shahara wajen bai wa ‘yan ta’adda mafaka, waɗanda ke yawan kai matafiya hare-hare a kan titin Funtua zuwa Gusau.
Mutuwarsu ta zama babban ci gaba ga jami’an tsaro da ke aiki tuƙuru don tabbatar da zaman lafiya a yankin Arewa maso Yamma.
“Wannan babban ci gaba ne a yaƙin da muke yi da ɓarayin daji a Katsina da kewaye.
“Sojojin sama tare da haɗin gwiwar dakarun ƙasa za su ci gaba da kai wa maɓoyar ‘yan ta’adda hare-hare har sai an samu cikakken zaman lafiya,” in ji shi.