Cikar FRCN Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Jihohin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon
Published: 16th, March 2025 GMT
An yi kira ga gwamnatocin jihohin Arewacin Najeriya da su tabbatar da dorewar tashar Rediyon Nigeria (FRCN) Kaduna a matsayin abim tunawa da marigayi Firimiyan tsohuwar jihar Arewa, Alhaji Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto, ya bari.
Masu sauraron tashar sun yi wannan kira a cikin bayanai daban-daban yayin da suke tsokaci kan bikin cika shekaru 63 da kafuwar gidan rediyon a watan Maris na shekarar 1962.
Sun bayyana godiyarsu ga rawar da FRCN Kaduna ya taka tsawon shekaru duk da kalubalen aiki, wanda suka bukaci mahukunta su magance.
A sakon taya murna daban da suka aiko, Sanata Salisu Musa Matori, da Alhaji Umar Dembo, da Alhaji Umar Iya Gulak, da Alhaji Garba Baba da Alhaji Muhammad Damak Abubakar, sun jinjinawa gidan rediyon bisa bajintar da ya nuna, inda suka jaddada bukatar Gwamnatin Tarayya ta cika alkawuran da ta dauka na farfado da tashar.
Jami’in hulɗa da jama’a na Kungiyar Manoma ta Najeriya, Alhaji Muhammad Magaji, ya nuna matukar jin dadinsa kan yadda tashar ke tallafawa harkokin noma, zaman lafiya, hadin kai, da cigaban kasa. Yana mai kira da a cigaba da wannan yunkuri don cimma manufofin da aka sanya a gaba.
Daga Suleiman Kaura.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Shekaru 63
এছাড়াও পড়ুন:
Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto
Gwamnatin jihar Sokoto ta tabbatar da samun ɓullar cutar sanƙarau guda 300 a wasu ƙananan hukumomin jihar.
Kwamishinan lafiya na jihar Dakta Farouk Abubakar ne ya tabbatar da hakan a taron wayar da kan jama’a na kwana ɗaya da ƙungiyar raya unguwanni ta jiha (WDC) tare da haɗin gwiwar ma’aikatar lafiya ta jiha da hukumar kula da lafiya matakin farko ta jihar suka shirya a ranar Juma’a.
Darasi daga rayuwar Dakta Idris AbdulAzeez Dutsen Tanshi ’Yan bindiga sun harbe mata 2 a gona a KogiSai dai kwamishinan bai yi ƙarin bayani kan adadin mace-macen da aka samu tun watan Fabrairu da aka fara samun ɓullar cutar ba.
Ya ce har yanzu mutane 16 na ci gaba da karɓar magani a asibitoci yayin da sauran kuma aka sallame su.
A jawabansu daban daban, mai ba da shawara na musamman kan harkokin kiwon lafiya a matakin farko na jiha, Dakta Muhammad Bello Marnona, da babbar sakatariyar hukumar, Dakta Larai Aliyu Tambuwal, sun yaba da irin hangen nesa na shugabancin hukumar ta WDC.
Sun ce, ana iya rigakafin cutar kuma sun shawarci mutane da su ziyarci cibiyoyin lafiya da ke kusa don samun magungunan da suka dace a duk lokacin da suka fuskanci wata matsala.
Shima da yake tsokaci shugaban yankin Malam Ya’u Muhammad Danda wanda mataimakinsa Alhaji Faruk Umar Garba ya wakilta ya bayyana taron a matsayin wanda ya dace.
A nasa jawabin, Sarkin Musulmi Sultan Sa’ad Abubakar wanda Hakimin Gagi, Alhaji Sani Umar Jabbi ya wakilta, ya yaba wa Gwamna Ahmed Aliyu da jagororin gwamnatinsa na inganta lafiyar al’umma.