An yi kira ga gwamnatocin jihohin Arewacin Najeriya da su tabbatar da dorewar tashar Rediyon Nigeria (FRCN) Kaduna a matsayin abim tunawa da marigayi Firimiyan  tsohuwar jihar Arewa, Alhaji Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto, ya bari.

Masu sauraron tashar sun yi wannan kira a cikin bayanai daban-daban yayin da suke tsokaci kan bikin cika shekaru 63 da kafuwar gidan rediyon a watan Maris na shekarar 1962.

Sun bayyana godiyarsu ga rawar da FRCN Kaduna ya taka tsawon shekaru duk da kalubalen aiki, wanda suka bukaci mahukunta su magance.

A sakon taya murna daban da suka aiko, Sanata Salisu Musa Matori, da Alhaji Umar Dembo, da Alhaji Umar Iya Gulak, da Alhaji Garba Baba da Alhaji Muhammad Damak Abubakar, sun jinjinawa gidan rediyon  bisa bajintar da ya nuna, inda suka jaddada bukatar Gwamnatin Tarayya ta cika alkawuran da ta dauka na farfado da tashar.

Jami’in hulɗa da jama’a na Kungiyar Manoma ta Najeriya, Alhaji Muhammad Magaji, ya nuna matukar jin dadinsa kan yadda tashar ke tallafawa harkokin noma, zaman lafiya, hadin kai, da cigaban kasa. Yana mai kira da a cigaba da wannan yunkuri don cimma manufofin da aka sanya a gaba.

 

Daga Suleiman Kaura.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Shekaru 63

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Da Bankin Duniya Sun Dauki Nauyin Dalibai 500 A Fannin Fasahar Zamani

Gwamnatin Jihar Jigawa, tare da hadin gwiwar Bankin Duniya, ta dauki nauyin dalibai sama da 500 a wani mataki na tsara makomar matasa a fannin fasahar zamani.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan yayin bikin kaddamar da shirin da kuma mika takardun shaidar karatu ga wadanda suka ci gajiyar shirin fasahar zamani na Innovation Development and Effectiveness in the Acquisition of Skills (IDEAS) a Jihar Jigawa.

Malam Umar Namadi ya jaddada kudirin gwamnatinsa na karfafawa matasa ta hanyar kirkire-kirkire a fannin fasahar zamani da kuma koyon sana’o’i don habaka tattalin arziki.

“A yau, mun kammala horar da dalibai 240 da suka koyi yadda za su bunkasa  harkokinsu na kasuwanci don tabbatar da ci gaba mai dorewa,” in ji gwamnan.

“Haka kuma, a yau muna mika takardun shaidar karatu ga dalibai 550 da suka sami guraben karatu ta hannun Hukumar Samar da Ayyuka da Taimakon Matasan Jihar Jigawa, tare da hadin gwiwar Bankin Duniya, Arms of Ideas, da gwamnati.”

A cewarsa, wadannan dalibai da suka sami guraben karatu a Jami’ar Baze za a horas da su a fannonin fasahar zamani da ke taka muhimmiyar rawa a kasuwannin duniya.

Gwamna Namadi ya bayyana cewa karkashin wannan shiri, Gwamnatin Jihar Jigawa da Bankin Duniya sun saka hannun jarin sama da Naira miliyan 100 domin tabbatar da samun ingantaccen ilimi da koyon sana’o’i.

“Wannan kudade hadin gwiwa ne tsakanin Bankin Duniya da Gwamnatin Jihar Jigawa. Bankin Duniya ya bayar da Naira miliyan 85, yayin da gwamnatin jihar ta bayar da Naira miliyan 50, kuma an riga an biya kudaden gaba daya.”

Ya kara da bayanin cewa shirin zai ba dalibai damar koyon akin binciken sirri, (Artificial Intelligence), da fasahar blockchain, binciken kasuwanci (Business Intelligence), da tsaron yanar gizo (Cybersecurity), da sauransu.

Baya ga horon fasahar zamani, gwamnan ya kuma sanar da kammala horas da matasa ‘yan kasuwa 240 da suka samu horo kan hanyoyin bunkasa kasuwancinsu. Ya kara da cewa kowannensu zai samu tallafin jari na Naira 50,000 domin fadada kasuwancinsu da kuma tabbatar da dorewarsa.

Saboda haka, Gwamna Namadi ya bukaci daliban da su yi amfani da wannan dama yadda ya kamata, tare da tabbatar musu da karin tallafi ga wadanda suka yi fice a karatunsu.

“Ina bukatar ku yi kokari don cimma wannan buri. Duk wani dalibi da ya kammala karatu da Upper Credit ko Distinction zai samu sabuwar kwamfutar tafi-da-gidanka (laptop) domin tallafa masa!”

Ya sake tabbatar da goyon bayan gwamnatinsa ga fannin fasahar zamani,  da karfafawa matasa tattalin arziki a Jihar Jigawa, tare da alkawarin gabatar da karin manufofi da shirye-shirye don inganta rayuwarsu da kuma bunkasa sana’o’insu.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cikar FRCN Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Jihohin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon
  • Hamas ta yi Allah wadai da haramcin da Amurka da EU suka yi wa gidan talabijin na Al-Aqsa
  • Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Gwamnatin Jigawa Da Bankin Duniya Sun Dauki Nauyin Dalibai 500 A Fannin Fasahar Zamani
  • ‘An Kwashe Shekaru Ana Kashe Kudaden Yaran da ba a ma Haife su ba a Nijeriya’
  • 2027: An Buga Gangar Neman Tazarcen Tinubu A Arewa
  • Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500
  • ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3
  • Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai