Cikar FRCN Kaduna Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon
Published: 16th, March 2025 GMT
An yi kira ga gwamnatocin jihohin Arewacin Najeriya da su tabbatar da dorewar tashar Rediyon Nigeria (FRCN) Kaduna a matsayin abim tunawa da marigayi Firimiyan tsohuwar jihar Arewa, Alhaji Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto, ya bari.
Masu sauraron tashar sun yi wannan kira a cikin bayanai daban-daban yayin da suke tsokaci kan bikin cika shekaru 63 da kafuwar gidan rediyon a watan Maris na shekarar 1962.
Sun bayyana godiyarsu ga rawar da FRCN Kaduna ya taka tsawon shekaru duk da kalubalen aiki, wanda suka bukaci mahukunta su magance.
A sakon taya murna daban da suka aiko, Sanata Salisu Musa Matori, da Alhaji Umar Dembo, da Alhaji Umar Iya Gulak, da Alhaji Garba Baba da Alhaji Muhammad Damak Abubakar, sun jinjinawa gidan rediyon bisa bajintar da ya nuna, inda suka jaddada bukatar Gwamnatin Tarayya ta cika alkawuran da ta dauka na farfado da tashar.
Jami’in hulɗa da jama’a na Kungiyar Manoma ta Najeriya, Alhaji Muhammad Magaji, ya nuna matukar jin dadinsa kan yadda tashar ke tallafawa harkokin noma, zaman lafiya, hadin kai, da cigaban kasa. Yana mai kira da a cigaba da wannan yunkuri don cimma manufofin da aka sanya a gaba.
Daga Suleiman Kaura.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Shekaru 63
এছাড়াও পড়ুন:
Ramadan Iftar: Sarkin Kauru Ya Hori Al’umma Su Hada Kai Su Zauna Lafiya da Juna
Mai Martaba Sarkin Kauru dake Jihar Kaduna Alhaji Zakari Ya’u Usman ya bukaci samun hadin kai da aiki tare kana da hakuri da juna tare da ɗaukar banbance banbance dake tsakanin al’umma a matsayin wata baiwa.
Alhaji Zakari Ya’u II yayi wannan horonne lokacin da aka taru a fadarsa dake Kauru domin shan ruwan azumin Ramadan.
Mai martaban ya bayyanawa wadanda suka taru domin wannan aikin lada na shekara shekara cewa, akwai bukatar yafiya da ‘yan uwantaka a wannan lokaci na Ramadan tare da godiya ga Allah da ya sake nuna mana wannan watan mai albarka.
Alhaji Zakaria Ya’u Usman yace akwai bukatar sadaukarwa da mika wuya ga Allah da kankantar da kai tare da fahimtar cewa wannan banbanci da ke tsakanin al’umma wata baiwa ce daga huwallazi tare da kira ga jama’a su nuna godiya ga Allah da wannan baiwar.
Yace Allah baya kuskure, saboda haka mu dauki wannan banbancin dake tsakanin mu a matsayi wata hanya ta aiki tare da nuna karfin mu na zama al’umma daya.
Sarkin Kauru ya godewa gwamnan jihar Kaduna Uba Sani saboda samarda zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kaduna tare da gamsuwa da yunkurin karamar hukumar Kauru da jami’an tsaron wajen samar da kwanciyar hankali musamman kalubalen tsaron da wasu miyagun mutane suke haddasa wa a yankin.
Ganin yadda bukukuwan sallah ke karatowa, mai martaba ya hori talakawansa su kasance masu riko da kyawawan dabi’u da yafewa juna tare da tunatar da su cewa watan Ramadan ba wai ana magana akan azumi ne kadai ba, akwai bukatar ganin sa a ayukkan mu na yau da kullum.
Haka Kuma, sakataren masarautar Muhammad Sani Suleiman (Dan Buran Kauru) ya nanata kudurin masarautar na samarda zaman lafiya da hadin kai tsakanin al’ummar yankin.
Radio Nijeriya Kaduna ya bada labarin cewa an kammala wannan bikin shan ruwa na masarautar Kauru da gudanar da addu’o’in samun zaman lafiya da ci gaban al’ummar yankin a daidai lokacin da ake shirin bukukuwan sallah.
Yusuf Zubairu Kauru