Aminiya:
2025-03-16@20:26:56 GMT

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina

Published: 16th, March 2025 GMT

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe ’yan bindiga 31 tare da lalata sansaninsu a Jihar Katsina, yayin wasu hare-hare guda biyu da suka kai.

A farmaki na farko, dakarun Operation Fansan Yamma sun yi artabu da ’yan bindiga a garin Maigora da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.

Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka

Da farko, sojojin sun kashe ’yan bindiga biyar bayan sun kai farmaki garin.

Sai dai lokacin da suka sake haɗuwa don kai harin ramuwar gayya, sojojin sun sake kashe guda bakwai, ciki har da Dogo, wanda babban Kwamanda ne a cikinsu.

Haka kuma, sojojin sun ƙwace babura guda bakwai da ‘yan bindigar ke amfani da su.

A wani farmakin, rundunar sojojin sama ta yi luguden wuta a maboyar ’yan bindiga da ke dajin Unguwar Goga, Ruwan Godiya, a Ƙaramar Hukumar Faskari.

Sun lalata sansanin shugabannin ’yan bindiga biyu; Alhaji Gero da Alhaji Riga, inda suka kashe aƙalla mahara 19.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa sojojin Najeriya na ƙara ƙaimi wajen murƙushe ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma, tare da lalata sansaninsu.

Har ila yau, sojojin na ci gaba da sintiri ta sama da ƙasa don daƙile yunƙurin ’yan bindiga na sake hare-hare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga dakaru hare hare yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

 Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki

A jiya juma’a ne dai firma ministan kasar Iraki Muhammad Shi’ya al-Sudani ya sanar da cewa sojojin kasar sun kashe babban dan ta’adda Abdullahi Makki wanda ake yi wa lakabi da Abu Hadiza.

Al-Sudani ya kara da cewa; Iraki taba cigaba da samun nasara akan ‘yan ta’adda, bayan da jami’an tsaro na kasa da kasa su ka yi nasarar kashe Abdullahi al-makki, wanda ya kasance a matsayin  mataimakin shugaban abind ake kira da Daular Musulunci a Iraki da Syria.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fiye Da Mutane 20 Ne Su Ka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren  Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
  • An kama malama tana lalata da ɗalibinta
  • ’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina
  •  Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
  • Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina 
  •  Sojojin Kungiyar  “SADC” Sun Janye Daga DRC
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • HKI Tana Cigaba Da Keta Tsagaita Wutar Yaki A Lebanon
  • Sojoji sun ceto mutum 7 daga hannun ’yan bindiga a Filato