HausaTv:
2025-03-16@21:09:17 GMT

Trump Ya Dakatar Da Kafar Watsa Labarai Ta VOA

Published: 16th, March 2025 GMT

Sama da shekaru 80 kenan da kafa VOA wadda ke yada shirye-shiyenta cikin harsuna 40.

Shugaba Donald Trump na Amurka ya ba da umarnin dakatar da ayyukan wasu hukumomin ƙasar guda shida da rushe wasu baki daya, ciki har da kafar yaɗa labarai ta Voice of America wato VOA.

Sauran hukumomin sun hada da gidajen adana kayan tarihi da ɗakunan karatu da bangaren kula da marasa galihu da ke kwana kan tituna.

Daga ciki har da hukumar US Agency for Global Media wadda gidan rediyon Muryar Amurka wato VOA ke karkashinta da Radio Free Europe da Asia da Radio Marti wadda ke yaɗa labarai da Sifaniyanci a Cuba.

Haka kuma tuni Trump din ya soma daukar wasu matakai wadanda suka hada da soke kwantiragin da VOA din ke da shi na amfani da labaran kafafen watsa labarai masu zaman kansu daga ciki har da kamfanin dillancin labarai na Amurka wato AP.

Daraktan Muryar Amurka, Mike Abramowitz, ya ce an aike kusan dukkanin ma’aikatan hutun dole na sai baba ta gani.

Sannan kudaden da ake warewa wajen tafiyar da kafofin da ke karkashinta, irinsu Gidan Rediyon Turai da Asia da kuma Liberty an dakatar da su baki daya.

Babu dai wani takamaiman bayani daga gwamnatin Amurka kan me hakan ke nufi, sannan babu wanda zai iya fahimtar ko an rufe kafofin baki daya ke nan.

Tuni dai Shugaba Trump ya nada ’yar jarida Kari Lake a matsayin daraktar hukumar da za ta kula da rushe wadannan hukumomi, wadanda ya zarga da yada labaran nuna masa kiyayya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya ce ya karbi  wata wasika daga shugaban kasar Amurka Donald Trump ta hannun manzon kasar Hadaddiyar Daular Larabawa.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Instagram, Araghchi ya bayyana cewa, na karbi bakuncin Anwar Gargash mai baiwa shugaban kasar Hadaddiyar Daular Larabawa shawara kan harkokin diflomasiyya. Baya ga tattaunawa kan huldar dake tsakanin kasashen biyu da kuma batutuwan yankin, na samu wasikar shugaban kasar Amurka.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana cewa, tuni aka mika wannan wasika ga jagoran juyin juya hali domin yin nazari a kanta, da kuma daukar matakin da ya dace dangane da wasikar.

Wasu bayani na cewa wasikar dai tana kunshe ne da wani sako da ke neman Iran da ta shiga tattaunawa kai tsaye tare da Amurka dangane da batun shirinta na nukiliya.

A baya dai Trump da kansa ya yi ikirari a wata hira da Fox Business cewa ya aike da wasika zuwa ga jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

Jami’ai daban-daban na Iran ciki har da Araghchi, sun yi watsi da ikirarin na Trump.

Baya ga haka kuma Iran ta sha nanata cewa ba za ta shiga duk wata tattaunawa da amurka a karkashin matsin lamba ko barazana ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka Ta Kudu Ta Caccaki Amurka Kan Korar Jakadanta Daga Washington
  • Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka
  • Trump ya dakatar da kafar watsa labarai ta VOA
  • Trump ya rushe kafar watsa labarai ta VOA
  • Gwamnatin Trump na tunanin hana ‘yan kasashe kusan 40 ciki har da Iran shiga Amurka
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  • Wadda ke damfara da sunan matar gwamnan Katsina ta shiga hannu
  • Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta