HausaTv:
2025-03-16@21:09:17 GMT

Afirka Ta Kudu Ta Caccaki Amurka Kan Korar Jakadanta Daga Washington

Published: 16th, March 2025 GMT

A ranar Juma’a ce Amurka ta bai wa Jakadan Afirka ta Kudu, Ebrahim Rasool, wa’adin sa’o’i 72 ya tattara komatsai ya fice daga ƙasar.

Hakan na kunshe cikin wata ’yar takaitacciyar sanarwa da mai magana da yawun ma’iakatar harkokin wajen Amurka, Chrispin Phiri ta fitar.

Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio ya zargi Ebrahim Rasool da kasancewa “dan siyasar wariyar launin fata mai kyamar Amurka,” lamarin da ya kara rura wutar rikicin diflomasiyya da ya kunno kai tsakanin Washington da Pretoria.

A cikin watan Fabarairun da ya gabata ne Shugaba Donald Trump ya wallafa wani saƙo a shafinsa na sada zumunta na Truth Social cewa Amurka ta dakatar da duk wani tallafi da take bai wa Afirka ta Kudu, sakamakon zarginta da ƙwace gonakin fararen fata na ƙasar.

Wannan dalili ne ya sa shugaba Trump ya sanar da cewa duk wani manomi da aka kwace wa gona, kuma yake fatan koma wa Amurka to zai samu izinin zama ɗan ƙasar cikin sauƙi.

Matakin da Amurka ta dauka na korar jakadan Afirka ta Kudu “abin takaici ne,” kamar yadda ofishin shugaban ƙasar Cyrill Ramaphosa ya bayyana a ranar Asabar, yana mai kira ga “gyara diflomasiyya” tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza

Gwamnatin da kuma mutanen kasar Somalia sun ki amincewa da shawarar shugaban kasar Amurka Donal Trump na korar Falasdinawa a Gaza zuwa kasar Somalia.

Shafin yanar Gizo na ‘Africa News’ ya nakalto yan kasar Somalia da dama suna fadar cewa yan kasar da kuma gwamnati ba zasu amince da korar Falasdinawa a Gaza, zuwa kasar Somalia kamar yadda shugaban kasar Amurka Donal Trump yake bada shawara ba.

Mohamed Mohamed Elmi Afrah daya daga cikin mutanen kasar Somalia wanda Shafin labarai na ‘Africa News’ yayi wa tambayoyi danganne da haka, yace: Ban tsamman cewa mutanen kasar Somalia zasu aminjce ba haka ma gwamnatin kasar.

Kafin haka dai wasu da dama suna ganin korar Falasdinawa daga Gaza ra’ayin yahudawan sahyoniyya ne, amma bayan da shugaban kasar Amurka Donal Trump wanda yahudawa suke  jujjuyawa ya gabatar da shi a fadar white House al-amarin ya sami maida martani mai tsananai daga shuwagabannin kasashen duniya. Da kuma kungiyoyin kare hakkin bil’adama.

Trump ta farko ya bada shawarar cewa kasashen Jordan da Masar su karbi mutanen Gaza, da suka ki sai ya koma kan sudan da Somaliya Somali landa da wasu kasashen kamar saudiya da sauransu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Ilimin Amurka Na Shirin Korar Ma’aikata 1,300
  • Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka
  • Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza
  • Nijar ta kori wasu kamfanonin China 3 daga ƙasar
  • Amurka Ta Ba Jakadan Afirka ta Kudu Sa’o’i 72 Ya fice daga kasar
  • Gwamnatin Trump na tunanin hana ‘yan kasashe kusan 40 ciki har da Iran shiga Amurka
  • Amurka Ta Ce Bata Bukatar Jakadan Kasar Afirka Ta Kudu A Kasar, Bayan Da Ya Aibata Shugaba Trump
  • Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya
  • Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta