IRGC: Iran ba za ta fara yaki ba amma za ta mayar da martani ga duk wata barazana
Published: 16th, March 2025 GMT
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya yi gargadin cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta taba neman wata kasa da yaki ba, amma kuma a lokaci guda ta shirya tsaf domin mayar da mummunan martani ga duk wata barazana ko shishigi daga makiya.
Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne a wannan Lahadi, bayan da Washington ta zargi Tehran da taimakawa sojojin Yaman a hare-haren da suka rika kaiwa haramtacciyar kasar Isra’ila a baya-bayan nan tare da yin kira da ta daina yin wanann zargi maras tushe balantana makama.
Salami ya ce, “Iran ba za ta taba zama mai fara yaki ba, amma idan aka fuskanci barazana, za ta mayar da martani mai tsanani.”
Shugaban kasar Amurka ya sake alakanta ayyukan da kungiyar Ansarullah ta Yaman ga Iran, ya kuma ce dole ne Iran ta daina goyon bayan kungiyar mai gwagwarmaya.”
Salami ya jaddada cewa, mutanen Yemen al’umma ce mai ‘yanci da ke bin manufofi na kashin kansu ba tare da an yi musu katsalandan ba. In ji babban kwamandan na IRGC.
Salami ya jaddada cewa, “Mu ba al’ummar da ke gudanar da ayyukanta cikin sirri ba ne; a maimakon haka, muna yin komai a bisa doka da oda da kuma kiyaye ka’idoji na duniya, kuma komai namua fili yake, kuma lokacin da muka dauki matakin soji a kan Isra’ila ba mu boye ma kowa ba kamar yadda duniya ta sheda hakan a cewar janar Salami.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Tace: Amurka Bata Da Hakkin Tsara Mana Yadda Zamu Tafiyar Da Kasar Mu
Ministan harkokin wajen kasar Iran y ace gwamnatin kasar Amurka bata da hakkin tsarawa kasar Iran yadda zata gudanar da manufofinta harkokin waje, wannan ya wuce tun bayana nasarar juyin juya hali musulunci a kasar a shekara ta 1979.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a shafinsa na X.
Aragchi yana maida martani ne ga shugaban kasar Amurka Donal Trump wanda ya tuta sojojinsa suka kai hare-hare kan kasar Yemen a jiya Asabar, don kada su hana jiragen ruwan HKI wucewa daga tekun Red Sea. Kuma ya ce: Ya gargadi Iran ta dakatar da tallafin da take bawa kungiyar Ansarullah. Don itace da alhakin duk abinda kungiyar take yi.
Ministan ya kara da cewa, ya maida martani da cewa: Amurka ce da alhakin marawa ayyukan ta’addancin da HKI take aikatawa a duniya, kuma gwamnatin shugaban Biden kadai ta kashe dalar Amurka biliyon 23 don kissan Falasdinawa kimani 60000 a Gaza. Don haka yana kira ga Amurka ta dakatar da tallafin da take bawa HKI wacce mafi yawan kasashen duniya ta dauketa a matsayin yar ta’adda.