Aminiya:
2025-03-17@00:09:19 GMT

An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa

Published: 16th, March 2025 GMT

An sanya dokar hana fita a Jihar Jigawa tare da kafa wuraren bincike domin magance matsalar rashin tsaro da ta biyo bayan kisan wata amarya mai shekaru 22, Zainab Ibrahim.

An yanke wannan shawara ne a taron da aka gudanar a Hadejia, wanda ya haɗa jami’an majalisar masarautar da hukumomin ƙananan hukumomin Malam Madori da Kirikasamma.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalma

Manufar taron ita ce samo mafita ga matsalolin tsaro da ke ƙara ta’azzara a yankin.

Da yake jawabi a madadin majalisar masarauta, Galadiman Hadejia, Usman Abdul’aziz, ya nuna damuwa matuƙa game da yawaitar hare-haren da ake kai wa jama’a.

Ya buƙaci shugabannin yankin da su haɗa kai da jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya.

An tsinci gawar Zainab Ibrahim, wacce aka ɗaura mata aure a baya-bayan nan, kwance cikin jini a gidanta da ke unguwar Warware.

Lamarin ya tayar da hankalin al’umma, lamarin da ya tilasta hukumomi ɗaukar matakan tsaro cikin gaggawa.

Bayan tattaunawa, an amince da sanya dokar hana fita daga ƙarfe 12 na dare zuwa 4 na Asuba, tare da kafa wuraren binciken tsaro.

Shugaban kwamitin tsaro na Ƙaramar Hukumar Hadejia, Ahmed Ari, ya bayyana cewa dokar hana fitar za ta taimaka wajen rage aikata laifuka da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Ya kuma roƙi al’ummar yankin su haɗa kai da jami’an tsaro domin tabbatar da nasarar waɗannan matakai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amarya Jigawa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’ar Gwamnatin Tarayya Kachia Ta Shirya Tsaf Domin Fara Aiki

Ya kara bayanin cewar Jami’ar za ta dauki sahun dalibanta na farko wato shekarar karatu ta 2025, inda ya kara jaddada aniyar gwamnati ta bada damar samun yin karatu na ilimi mai zurfi tare da bunkasa shi.

Ministan har ila yau ya ce zai taimaka wajen tabbatar da cewar Jami’ar ta samu nata kason daga Hukumar kula da ilimin manyan makaratun ta kasa, domin hakan zai taimakawa bunkasa Jami’ar cikin wani lokaci nan gaba.

Ya ci gaban da bayanin “Zan tabbatar da cewar Jami’ar ta samu taimako na gidauniya kula da ilimi mai zurfi ta lamurran manyan makarantu ta samun kudade daga wurinta wannan shekarar. Don haka wannan rana ce ta farin ciki ga al’ummar Kudancin Kaduna, al’ummar Jihar Kaduna, da kuma al’ummar Nijeriya baki daya kamar yadda ya furta maganar,” .

Da yake an mika satifiket din mallakar filin yanzu Gwamnatin tarayya c eke da mallakin filin da kuma Jami’ar, hakan kuma ya bada wata damar fara aikinta a Hukumance. “Filin yana da hekta fiye da 200 wanda yanzu Gwamnatin Jihar Kaduna ta mallakawa Gwamnatin tarayya ta hanyar ma’aikatar ilimi ta tarayya.Yanzu mune muke da takardar satifiket na mallakar Jami’ar,”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi
  • Yadda ango da ’yar uwar amarya suka rasu minti 30 kafin ɗaurin aure a Bauchi
  • Jami’ar Gwamnatin Tarayya Kachia Ta Shirya Tsaf Domin Fara Aiki
  • Zulum ya bai wa jami’an tsaro kyautar gidaje da motoci a Borno
  • Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai
  • Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo
  • Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar
  • Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi
  • Rasha ta caccaki gwamnatin Syria dangane da kisan kiyashin da jami’anta suke yi a kan tsiraru