El-Rufai ya nemi afuwa ko mu maka shi a kotu — Gidauniyar Ɗahiru Bauchi
Published: 17th, March 2025 GMT
Gidauniyar Sheikh Ɗahiru Bauchi ta buƙaci Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, da ya nemi afuwar ɗaliban malamin bisa abin da ta kira rashin adalci da aka musu.
Idan kuwa bai yi hakan ba kafin ƙarshen watan Ramadan, za su maka shi a kotu.
An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalmaWannan na ƙunshe ne a wata takarda da gidauniyar ta fitar, wadda Sayyadi Aliyu Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya sanya wa hannu.
A cewar takardar, dole ne El-Rufai ya fito ya yarda da laifinsa sannan ya nemi afuwar gidauniyar, ɗalibanta da jagoranta, Sheikh Ɗahiru Bauchi.
Gidauniyar ta zargi tsohon gwamnan da bayar da umarni ga jami’an tsaro don su kai samame a makarantun tsangayar Sheikh Ɗahiru Bauchi, inda aka kama wasu ɗaliban karatun Alƙur’ani har zuwa gidansa.
Har yanzu, akwai ɗaliban da ba a san inda suke ba.
Sayyadi ya bayyana cewa an yi hakan ne da gangan domin a tozarta Sheikh Ɗahiru Bauchi da kuma hana ci gaban ilimin addini da ya ke yi.
Ya ce idan har El-Rufai bai nemi afuwa ba kafin ƙarshen Ramadan, za su kai ƙararsa ga Shugaban Ƙasa, ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam, da kotu.
Idan kuwa duka ba su yi musu adalci ba, za su mika ƙarar ga Allah ta hanyar addu’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gidauniya Neman Afuwa Sheikh Ɗahiru Bauchi Sheikh Ɗahiru Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
A wannan rana a filin jirgin saman Legas, Babafemi ya ce jami’an ‘yansanda sun kama wata ‘yar asalin kasar Ghana mai shekaru 20, mai suna Parker Darren Hazekia Osei, mai shekaru 20 da haihuwa, dauke da fakiti 36 na Loud—wani nau’in tabar wiwi mai karfin gaske, a cikin wata katuwar jakar tafiya mai nauyin kilogiram 19.40.
Ya ce wanda ake zargin wanda ya bayyana kansa a matsayin dalibin Kimiyyar Kwamfuta a Jami’ar Gabashin Landan, ya taso ne daga birnin Bangkok na kasar Thailand ta hanyar jirgin Ethiopian Airlines, ya kuma amince ya dauko kayan a Bangkok domin kai wa Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp