Angola Ta Bukaci Tsagaita Wuta Kafin Taron Zaman Lafiya Tsakanin Kongo Demokradiyy Da Kungiyar M-23
Published: 17th, March 2025 GMT
Shugaban kasar Angolan João Lourenço, wanda kuma shi ne ke rike da shugabancin karba-karba na kungiyar tarayyar Afirka (AU) ya yi kira ga gwamnatin Congo Democradiyya da mayakn M-23 su kawo karshen yaki kafin taron tattauna batun tsagaita wuta a gabacin kongo nan gaba.
Shafin yanar gizo na labarai ‘Afirca News” ya nakalto shugaban yana kira ga bangarorin biyu su tsagaita wuta da misalign tsakiyar daren jiya Lahadi don a tattauna batun samar da zaman lafiya cikin Nutsuwa.
Majiyar fadar shugaba Lourenco na cewa yakamata tsagaita wutan ya hada har da rashin kokarin mamayar karin iko a wasu wurare. Da kuma dakatar da fada. Da kashe fararen hula da sauransu.
An shiya cewa gwamnatin kongo Democradiyya da kuma wakilan yan tawayen M-23 zasu hadu a karon Farko don tattauna batun tsagaita budewa Juna wuta da kuma kawo karshen yakin a ranar 18 ga watan Maris, wato gobe talata , a birnin Luanda babban birnin kasar ta Angola.
Gwamnatin Kongo Democradiyya dai bata bayya a fili zata halarci taron sulhun wanda kasar Angola ta shirya ba, amma M-23 ta nuna goyon bayanta ga shirin na kasar Angola. Sai dai ta yikira ga shugaba Tsetsekedi ya bayyana anniyarsa ta zuwa taron sulhun a fili.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin Ta Gabatar Da Shawarwarin Warware Batun Nukiliyar Iran
Na hudu, kudurin Sin shi ne inganta hadin gwiwa ta hanyar tattaunawa, tare da adawa da neman kwamitin sulhu na MDD ya shiga tsakani.
Bugu da kari, ministan ya ce Sin za ta tsaya kan dabarar daukar matakai daya bayan daya da saka alheri da alheri, da neman cimma matsaya ta hanyar tattaunawa. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp