Kungiyar Ansarullah Ta Ce Keta Hurumin Kasar Da Amurka Ta Yi Zai Gamu Da Maida Martani
Published: 17th, March 2025 GMT
Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Abdulmalik Badruddeen Huthi ya bayyana cewa hare-haren ta’adanci wadanda sojojin Amurka da Burtaniya suka kai kan yankuna da dama a kasar ba zasu hana mutanen kasar ci gaba da kare Falasdinawa a Gaza ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Al-huthi yana fadar haka a wani jawabin da ya gabata a jiya Lahadi da yamma.
Kafin haka dai jiragen saman yakin wadanda suka taso daga kan kataparen jirgin ruwa mai daukar Jiragen yaki na kasar Amurka sun kai hare hare a yankuna da dama a kasar ta Yemen wadanda suka hada da birnin San’a babban birnin kasar. Hare-haren dai sun kashe yara da mata da dama sannan sun lalata injunan wutan lantarki da dama.
Kungiyar Ansarullah ta kasar yemen dai ta tallafawa Falasdinawa a yankin tufanul Aksa wanda aka fara a ranar 7 ga watan octoban shekara ta 2023. Har zuwa lokacin da aka tsagaita wuta a ranar tsakanin Falasdinawa a Gaza da HKI a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025.
Amma a cikin yan makonnin da suka gabata HKI ta hana abinci da magunguna da kuma sauran bukatun Falasdinawa shiga yankin na Gaza. Wanda ya sa kungiyar ta koma tana hana jiragen HKI wucewa ta Tekun maliya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila
Wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta ba da fifiko wajen dakatar da hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi wa kasar Labanon.
A cewar Al-Mayadeen Hassan Fadlallah mamba a bangaren Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon ya ce: Dakatar da wuce gona da iri kan kasar Labanon wani muhimmin al’amari ne na kasa da ya zama wajibi a sanya shi cikin ajandar gwamnatin Lebanon.
Ya kara da cewa: Al’ummar kasar Labanon suna fuskantar wuce gona da iri na gwamnatin sahyoniyawan tare da yin kira ga gwamnati da ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na dakile wannan ta’addanci.
Fadlallah dai ya dauki babbar matsalar kasar Labanon a matsayin mamaya da kuma keta hurumin kasar, yana mai jaddada cewa wasu na son jefa kasar cikin rudani da ruguza karfin da kasar ta Lebanon ke da shi na tunkarar mulkin kama-karya na kasashen waje. Irin wadannan ayyuka sun saba wa muradun kasar Lebanon, kuma sun yi daidai da muradin makiya.
Hassan Fadlallah ya musanta ikirarin da wasu kafafen yada labarai suka yi cewa Hizbullah na amfani da tashar jiragen ruwa na Beirut wajen safarar makamai, ya kuma yi kira ga mahukuntan kasar Lebanon da su dauki mataki kan masu yada wadannan karairayi.