Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwon Gargajiya ta Afrika wato CORET, tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika ECOWAS, sun bayyana shirinsu na samar da ayyuka guda dubu uku ga matasa ta hanyar sarrafa madara a sarkar darajar madara a Jahohin Kaduna da Jigawa.

 

Shugaban Shirin na CORET, Dr.

Umar Hardo, ne ya bayyana hakan yayin taron horaswa da ƙungiyoyin haɗin kai Sha biyu da aka zaɓo wanda ya gudanar a yankin Ladduga dake ƙaramar hukumar Kachia a Jihar Kaduna.

Taron horaswar na tsawon kwanaki biyu ya haɗa shugabanni daga ƙungiyoyin kiwo na madara guda goma sha biyu, masu tara madara, da shugabannin al’umma. Wannan shiri da ECOWAS ta ɗauki nauyi, zai fara aiki gwaje ne a ƙauyuka biyu, a Ladduga a Jihar Kaduna da kuma Maigatari a Jihar Jigawa.

 

Haka kuma, an samu goyon baya daga Hukumar Ci gaban Kasar Sweden, inda ake aiwatar da aikin ta hanyar haɗin gwiwar wasu ƙungiyoyi kamar Hukumar Kula da Makiyaya da kuma da sauran su.

 

Dr. Umar Hardo ya bayyana cewa taron horaswar na nufin bai wa ƙungiyoyin haɗin kai horo da ilimi a duk fannoni na samar da madara domin cigabansu

 

“CORET ta riga ta shiga haɗin gwiwa da kamfanoni irin su Milk Copal, Nestlé da Farm Fresh. Kuma an gina cibiyoyin tarin madara masu amfani da hasken rana a Ladduga da Maigatari,” in ji shi.

 

Dr. Umar Hardo ya ƙara da cewa an tsara horaswar ne akan matasa dari huɗu, amma matasa dari tara da ashirin da uku daga Ladduga suka nuna sha’awar shiga, lamarin da ya nuna yadda matasa ke da sha’awar shiga ƙungiyoyin haɗin gwiwa.

Ya ce daga cikinsu, an zaɓi matasa dari huɗu daga Maigatari, Jihar Jigawa don samun horo a cikin shirin.

 

“CORET ta sanya hannu kan yarjejeniya da Ma’aikatar Noma ta Tarayya da kuma Ma’aikatun Noma na Jihohin Kaduna da Jigawa domin aiwatar da wannan aiki,” in ji shi.

 

Shugaban Shirin ya bayyana cewa wannan wani babban cigaba ne a tarihin Najeriya, domin wannan ne karon farko da ake gina cibiyoyin tara madara masu na’urorin sanyaya madara domin sauƙin jigilar ta ba tare da ta lalace ba.

 

Ya ƙara da cewa wani sashi na shirin, shi ne gina cibiyoyin tara madara tare da horas da mahalarta a matsayin masu tara madara daga karkara waɗanda za su kula da wadannan cibiyoyi da kuma ƙungiyoyin haɗin ksn.

 

A cikin Kasidarshi, Tsohon Darakta na Raya Al’umma da Ƙungiyoyin Haɗin Kai a Jihar Kaduna, Mista Yohanna Kabirat, ya ce horon ya mayar da hankali ne kan ƙungiyoyin haɗin Kai da gudanarwa, da shugabanci domin su gudanar da ƙungiyoyinsu cikin nasara.

 

Ya jaddada muhimmancin ƙungiyoyin haɗin kai wajen ci gaba mai ɗorewa ga membobinsu, musamman matasa na Ladduga.

 

Mista Kabirat ya shawarci mahalarta su isar da ilimin da suka samu ga sauran membobinsu, musamman wajen yin bayanawa kowa bayyanai ba tareda an boye ba wanda shi ne babban kalubalen da ya jefa ƙungiyoyi da dama cikin matsalolin kudi a baya.

 

Tsohon Daraktan a karshe yace tushen nasarar kowace ƙungiyar haɗin Kai shine bin dokokin ƙungiyar yadda ya kamata.

 

Da suke magana da Radio Nigeria Kaduna, wasu daga cikin mahalarta taron, Sufyanu Umar da Fatima Isa, sun bayyana farin cikinsu da horon da aka basu, inda suka ce sun samu ƙwarewa ta musamman wajen tafiyar da ƙungiyoyinsu cikin nasara da inganci.

 

Mahalarta taron horaswar sun yaba wa CORET da sauran abokan ci gaba bisa shirya taron horaswar da suka ce zai sauya rayuwarsu ta fannin samar da madara.

Sun bayyana cewa ilimin da suka samu zai kasance ginshiƙi mai ɗorewa ga rayuwarsu da ci gabansu.

 

Rahoto daga Adamu Yusuf.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ayyuka Jigawa Samarda

এছাড়াও পড়ুন:

Hasashen Samun Ruwan Sama A 2025: Shawarwarin Da Kwararru Suka Bai Wa Manoma

Saboda haka ne, hukumar ta shawarci manoman da ke da ra’ayin noma a kakar noman ta bana da su tabbatar sun tuntube ta, ko kuma tuntubar sauran hukumomin da ke hasashen yanayi, domin sanin lokacin da ya ya fi dacewa su yi shuka.

Hukumar ta yi hasashen cewa, jihohin Zamfara, Katsina, Kano, Kaduna, Jigawa, Filato, Bauchi, Borno, Yobe, Adamawa, Taraba, Neja, Kwara, Kogi, Abuja, Ekiti da kuma Ondo, za su fuskanci daukewar ruwan sama da wuri, inda aka kwatanta da na dogon zango da aka samu a daminar bara.
Haka zalika, hukumar ta yi hasashen cewa; za a samu jinkirin ruwan sama a wasu sasssan jihohin Kaduna, Nasarawa, Benuwe, Legas, Kwara, Taraba, Oyo, Ogun, Kuros Riba, Delta, Akwa Ibom, Ebonyi, Anambra da kuma Enugu.

A cewar Hukumar, mai yiwuwa kakar daminar ta bana ta kasance gajera a wasu sassan Jihohin Borno da Yobe, sabanin yadda aka saba gani.

Hukumar ta yi hasashen cewa, mai yiwuwa kakar daminar ta bana, ta yi tsawo a Jihohin Legas da Nasarawa, sabanin yadda aka saba samu.

Hukumar ta yi hasashen cewa, daga watan Mayu zuwa na Yuni, za a samu ruwan sama kamar da baakin kwarya, wanda kuma mai yiwuwa, a samu afkuwar ambaliyar ruwa a wasu biranen da ke kusa da rafuka a kasar.
Kazalika, daga watan Afirilu zuwa na Mayu, yankunan Saki, Iseyin, Ogbomoso, Atisbo, Orelope, Itesiwaju, Olorunsgo, Kajola, Iwajowa da kuma Oro Ire da ke cikin Jihar Oyo, an yi hasashen samun karancin ruwan sama, wanda zai iya kai wa har tsawon kwana 15, bayan saukar ruwan saman.

Bugu da kari, Hukumar ta yi hasashen cewa; a wasu jihohin da ke Arewacin kasar nan, daga watan Yuni zuwa Yuli har zuwa watan Agustan 2025, za a samu karancin ruwan sama, wanda zai kai har tsawon kwana 21, inda kuma a Jihohin Ekiti, Osun, Ondo, Ogun, Edo, Ebonyi, Anambra, Imo, Abia, Kuros Riba, Delta, Bayelsa da kuma Akwa Ibom, za a samu ruwan sama na tsaka-tsaki da zai kai kwana 15.

Daga tsakanin kwana 27 zuwa 40, za su shige ba tare da wani batun hasashe samun sauyin yanayi ba, haka za a fuskanci rani kadan a yankin Kudu Maso Gabas daga ranar 22 na 2025.

Saboda haka ne, kwararru a fannin aikin noma suka shawarci manoman kasar nan, musamman wadanda ke jihohin da ke tsakiyar kasar, da su tabbar da sun yi shuka da Irin da ke jurewa kowanne irin yanayi, musamman domin kauce wa fuskantar matsalar rashin samun saukar ruwan sama a kan lokaci a kakar noman ta 2025.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa
  • Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci
  • Hasashen Samun Ruwan Sama A 2025: Shawarwarin Da Kwararru Suka Bai Wa Manoma
  • Jami’ar Gwamnatin Tarayya Kachia Ta Shirya Tsaf Domin Fara Aiki
  • Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  •  Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14
  • Na Cire Tallafin Mai Ne Domin Kare Makomar Matasan Nijeriya —Tinubu
  • Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas
  • Gwamnatin Jigawa Da Bankin Duniya Sun Dauki Nauyin Dalibai 500 A Fannin Fasahar Zamani