Aminiya:
2025-04-13@09:47:06 GMT

Tsohuwar ɗaliba ta kai ƙarar makarantar da ta kammala

Published: 17th, March 2025 GMT

Wata matashiya mai suna Aleysha Ortiz ’yar shekara 19 da ke Jihar Connecticut a Amurka ta dauki matakin shari’a a kan tsohuwar makarantar sakandaren gwamnatin da ta yi saboda gazawarta ta hanyar ba ta damar kammala karatu “da sakamako mai daraja” duk da ta kasance maras ƙoƙari.

A watan Yunin shekarar bara ce, Aleysha Ortiz ta kammala karatu a Makarantar Hartford Public High School da ke Hartford, a Jihar Connecticut, inda aka karama ta, har ma ta samu gurbin karatu a kwaleji, amma yanzu ta kai karar tsohuwar makarantarta saboda sakacinta.

Gidauniyar Dangote ta ƙaddamar da rabon abincin N16bn ga talakawan Nijeriya EFCC ta kama Murja Kunya kan wulaƙanta takardun Naira

Matashiyar mai shekara 19 tana zargin makarantar da ta kammala da yin watsi da karatunta, tana mai cewa da ƙyar za ta iya riƙe fensir a hannunta kuma ƙoƙarin karatunta ya yi kama da na dalibi ɗan aji daya.

An haife ta a garin Puerto Rico, Aleysha tana fama da matsalolin koyo tun tana karama, kuma dabi’arta ta ci gaba bayan ta yi ƙaura zuwa Amurka tana ’yar shekara 5.

Ta yi iƙirarin cewa, makarantarta da kuma malaminta na musamman da aka ba ta ba su da wani amfani har sai wata guda kafin ta kammala karatunta a zango na ƙarshe lokacin da suka gudanar da ƙarin gwajin da take nema kuma suka gane cewa ba ta da ƙoƙari.

Jami’an hukumar makarantar sun shaida wa matashiyar cewa, za ta iya jinkirta karɓar takardar shaidar kammala karatunta na difiloma don sauya su da wasu ayyuka. Amma ta ƙi amincewa.

Ortiz ta bayyana wa CNN cewa, “Na yanke shawarar shigar da ƙara, yanzu lokacina ne,” inda ta ƙara da cewa, kammala karatunta da karramawa daga makarantar sakandare Hartford Public High School, wanda yawanci yana nufin ɗalibi ya nuna ƙwarewa a fannin ilimi.

Amma ta yaya Aleysha Ortiz za ta kammala karatun sakandare tare da karramawa yayin da ba ta iya karatu da rubutu ba? Ta yaya aka karɓe ta zuwa Jami’ar Connecticut?

Ta yi iƙirarin cewa, manhajojin zamani suna matuƙar taimakawa. Tana amfani da manhajojin wayar hannu don fassara rubutu zuwa murya da murya zuwa rubutu, har ma ta yi amfani da su wajen aikace-aikacen kwalejin da rubuce-rubucen da ake bukata. Kasancewarta ɗalibai kwalejin ya saka ta cikin yanayi na daban-daban.

Aleysha ta yarda cewa, inda ta daina zuwa ajin karatu a farkon Fabrairu. Ta so ta ɗauki lokaci don kula da lafiyar ƙwaƙwalwarta, amma tana fatan komawa azuzuwa nan ba da jimawa ba.

Aleysha ta ce, ta kai ƙarar tsohuwar makarantarta ce saboda tana son a tuhumi shugabanninta kan abin da ta fuskanta.

Ta yi ikirarin cewa, “ba su san abin da suke yi ba kuma ba su damu ba,” kuma tana fatan cewa, fafutukar da take yi a shari’ar zai hana wasu matasa rashin samun cikakken ilimi.

“Ni mutum ce mai matukar sha’awar karatu kuma ina son koyo,” in ji Ortiz.

“Mutane sun yi amfani da wannan damar don koyo, kuma yanzu ina kwaleji kuma ina so in yi amfani da wannan.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaliba Makaranta kammala karatu

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ya janye harajin da ya kara wa duniya, amma ya laftawa China 125%

Shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da haraje-harajen da ya lafta kan kayayyakin da ke shiga kasar daga kasashen duniya, sai dai ya kara harajin da kashi 125 ga kasar China.

A wani bayani da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Shugaba Trump ya ce za a rage haraje-harajen zuwa kashi 10%, sai dai za a kara wanda aka lafta kan kayan China zuwa kashi 125%.

Donald Trump ya kuma zargi China da nuna rashin girmamawa da kuma zaluntar Amurka.

Kafin haka, China ta sanar da kara haraji kan kayan Amurka da ake shiga da su kasarta zuwa kashi 84% – inda Chinar ta zargi Amurka da barazana kan kasashen duniya.

Matakin na zuwa ne jim kadan bayan da Beijing ta mayar da martani ga karin harajin da Washington ta yi a baya

Trump ya kuma yi nuni da cewa, ba kamar China ba, “wadannan kasashen, bisa ga kwakkwarar shawarata, ba su mayar da martani ta kowace hanya, ko siffa, a kan Amurka ba.”

Kazalika, jami’an Amurka sun bayyana a wannan rana cewa, yanzu kasashe ko kungiyoyin kasa da kasa fiye da 50 sun riga sun tuntubi Amurka kan matakin nata na harajin kwastam.

Wannan lamarin ya shafi kasashe 70 na duniya, wani abu da ya haddasa barkewar rikicin kasuwanci tsakanin Amurkar da kasashe da dama, musamman manyan kasashen da take huldar kasuwanci da su, kamar China da kuma kasashen Tarayyar Turai.

Su ma kasashen Tarayyar Turai sun lafta harajin kashi 25 cikin dari kan kayan da Amurka da ake shiga da su yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • Najeriya Tana Fatan Samun Dalar Amurka Biliyan $200 A Ayyukan Sararin Samaniya
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (1)
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno
  • Trump ya janye harajin da ya kara wa duniya, amma ya laftawa China 125%
  • Ruwa Ya Ci Rayukan Mata Biyu A Kano