HausaTv:
2025-03-17@13:52:01 GMT

Shugaban Kasar Amurka Ya Kara Yawan Kasashen Da Ya Sa Wa Takunkumin Shiga Amurka

Published: 17th, March 2025 GMT

Shugaban kasar ta Amurka Donald Ttump ya kara yawan kasashen da ya sa wa takunkumin shiga cikin Amurka zuwa kasashe 43.

Daga cikin kasashen da ya sa wa sharuddan shiga cikin kasar Amurka sun hada guda 11 da su ne; Somaliya, Sudan, da Libya. Sai kuma Afghanistan, Cuba, Iran, Korea Ta Arewa, Syria, Venezuela da kuma Yemen.

A lokacin zangonsa na farko Trump matakin nasa ya ja hankalin duniya saboda yadda ya hana ‘yan hijira daga kasashen Iraki,  Libya, Somaliya, Sudan da Yemen shiga cikin kasar.

An kalubalanci matakin na shugaban kasar Amurka a wancan lokacin a kotu saboda yadda ya shafi mafi yawancin kasashen musulmi.

Bayan da Joe Biden ya zama shugaban kasa ya soke wancan matakin na Donald Trump a 2021.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Tehran a shirye take ta shiga tattaunawa da kasashen Turai bisa mutunta juna.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Araghchi da Ministan Harkokin Wajen Netherlands Caspar Veldkamp sun tattauna hanyoyin inganta alakar juna da sabbin abubuwa dake faruwa a yankin da na kasa da kasa.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya nanata tsarin kasar na kulla kyakkyawar alaka ta diflomasiyya da kasashen.

Iran da kasashen Turai dai na tattaunawar ba-zata kai a kai tun shekara ta 2021, shekaru uku bayan da Amurka ta fice daga yarjejeniyar nukiliyar iran – tare da maido da takunkumin da Washington ta kakaba wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

bangarorin kasashen Turai da suka shiga yarjejeniyar nukiliya – Birtaniya, Faransa da Jamus – sun kasa cika alkawarin da suka dauka na dawo da Washington cikin yarjejeniyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Yaba Da Yarjeniyar  Zaman Lafiya Da Aka Cimma Tsakanin Kasashen Armenia Da Azerbaijan
  • Kofar JMI A Bude Take Don Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza
  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  • Amurka Ta Ba Jakadan Afirka ta Kudu Sa’o’i 72 Ya fice daga kasar
  • Rasha Za Ta Kara Yawan Alkamar Da Take Kai Wa Kasashen Afirka
  • ’Yan Adawa Na Kitsa Makarkashiyar Tsige Ni – Akpabio
  • Kasashen Sin, Rasha Da Iran Sun Yi Kira Da Dakatar Da Matakin Kakaba Takunkumi Na Bangare Guda
  • Yadda Nijeriya Ta Zarce Yawan Man Da OPEC Ta Ware Mata – Bincike