Trump zai tuntuɓi Putin kan yaƙin Ukraine
Published: 17th, March 2025 GMT
Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce yana shirin tuntuɓar takwaransa na Rasha Vladimir Putin da zummar tattauna batun kawo ƙarshen yaƙin Ukraine.
Trump ya shaida wa manema labarai hakan a cikin jirgin shugaban ƙasa na Airforce One a kan hanyarsa ta zuwa Washington daga Florida cewa yana ƙoƙarin ganin cewa yaƙin ya zo ƙarshe.
Trump ya bayyana cewa an yi aiki sosai a game da kawo ƙarshen wannan rikici a cikin ƙarshen makon da ya gabata.
Trump na ƙoƙarin samun goyon bayan Putin a game da tayin tsagaita wuta na kwanaki 30, wanda Ukraine ta aminnce da shi a makon jiya.
Sai dai ana ci gaba da miƙa tayin ne a yayin da dukkannin ɓangarorin ke ci gaba da yi wa juna luguden wuta ta sama, har sai da sojin Rasha suka kusan fatattakar dakarun Ukraine a yankin Kursk.
A ranar Juma’a, Fadar Gwamnatin Rasha, Kremlin ta ce shugaba Putin ya aike da saƙo zuwa ga Trump a game da tsagaita wuta ta hannun manzon Amurka na musamman, Steve Witkoff, wanda ya ziyarci Moscow, inda yake bayyana aniyar tsagaita wuta amma da taka-tsantsan.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Yemen sun sha alwashin tsayin-daka kan barazanar Trump
Al’ummar kasar Yemen sun gudanar da wani gagarumin ganganmi a fadin kasar, inda suka lashi takobin tinkarar ta’addancin Amurka ta hanyar kara karfin soji, da hada karfi da karfe, da kuma abokan gaba shakat.
Gangamin ya zo ne bayan da jagoran gwagwarmayar kungiyar Ansarullah Abdul Malik al-Houthi ya bayyana cewa kasar a shirye ta ke duk wata barazanar Amurka.
“Ba mu tsoron kowa, kuma ba mu rusuna wa kowa sai Allah. Za mu fuskanci duk wani tashin hankali. ” inji shi
“A shirye muke mu tunkari dukkan azzaluman duniya ba tare da wata fargaba ko tsoro ba.
Abdul Malik al-Houthi ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya yi a ranar Lahadi, kwana guda bayan da Amurka ta kai wasu jerin hare-hare a Sanaa babban birnin kasar Yemen da wasu larduna da dama a fadin kasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama da suka hada da mata da kananan yara.
A yammacin ranar Asabar jiragen yakin Amurka da na Birtaniya sun kai hare-hare 47 a wurare da dama a Sanaa babban birnin kasar, da kuma wasu yankunan lardin Saada da ke arewacin kasar, da lardin al-Bayda da ke tsakiyar kasar, da kuma lardin Dhamar da ke kudu maso yammacin kasar, inda akalla mutane 31 sukayi shahada.