Aminiya:
2025-03-17@18:34:54 GMT

Majalisar Ribas ta soma shirye-shiryen tsige Gwamna Fubara

Published: 17th, March 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Ribas ta soma shirye-shiryen tsige Gwamna Similanayi Fubara daga muƙaminsa.

Hakan na ƙunshe cikin wata buɗaɗɗiyar wasiƙa mai cike da ƙorafi da majalisar ta fitar, inda take shirin tsige Gwamnan tare da mataimakiyarsa Farfesa Ngozi Odu.

Trump zai tuntuɓi Putin kan yaƙin Ukraine Madalla da hutu ga ’yan makaranta domin azumi

A cikin wasiƙar wadda take kafa hujja ta tanadin da Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya yi, ’yan majalisar sun zargin Gwamna Fubara da kashe kuɗaɗen jama’a ba bisa ƙa’ida ba.

Haka kuma, wasiƙar ta ce Gwamna Fubara ya hana majalisar gudanar da aikinta, da kuma naɗa mutane a muƙaman gwamnati ba tare da tantancewa ba.

Kazalika, tana tuhumar Gwamnan da ƙin biyan albashi da wasu alawus alawus da aka ware wa majalisar ciki har da dakatar da albashin Sakataren Majalisar, Emeka Amadi.

A bayan nan ne tsohon Gwamnan Ribas kuma Ministan Abuja mai ci, Nyesom Wike, ya ce ba zai hana majalisar sauke nauyin da rataya a wuyanta ba wajen tsige Gwamna Fubara.

A wata hira da manema labarai da ya gabatar ranar Laraba a Abuja, Mista Wike ya ce ’yan majalisar ba su yi laifi ba idan suka yanke shawarar tsige Fubara, saboda ya aikata laifukan da suka cancanci a tsige shi, ciki kuwa har da riƙe musu albashi na tsawon watanni.

Aminiya ta ruwaito cewa, tun bayan ’yan watanni da zama Gwamnan Ribas, aka sa zare tsakanin Fubara da Wike, inda har kawo yanzu rikicin siyasa a tsakanin ɓangarorin biyu ke daɗa ƙamari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokokin Ribas Siminalayi Fubara Gwamna Fubara tsige Gwamna

এছাড়াও পড়ুন:

Minista ya caccaki El-Rufai kan sukar Tinubu da APC

Ƙaramin Ministan Gidaje da Raya Birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya caccaki Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan sukar jam’iyyar APC da kuma Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A cikin wata sanarwa da hadiminsa, Seyi Olorunsola, ya fitar, ministan ya zargi El-Rufai da haddasa rikici saboda bai samu muƙamin minista ba.

Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina  Kotun ɗaukaka ƙara ba ta soke naɗin Sanusi II ba — Gwamnatin Kano

Ya ce tsohon gwamnan mutum ne da ƙware wajen haddasa ce-ce-ku-ce da kuma yanke tsauraran hukunci a harkokin siyasa.

Ata ya ce lokacin da El-Rufai yake gwamnan Kaduna, an samu matsaloli da suka haɗa da rashin tsaro, rikicin ƙabilanci da addini.

Ya kuma ce komawar El-Rufai jam’iyyar SDP wata hanya ce da yake ƙoƙarin amfani da ita don a ci gaba da dama da shi a fagen siyasa.

Ministan ya yi watsi da iƙirarin El-Rufai na cewa Tinubu yana haddasa rikici a jam’iyyun adawa, inda ya ce wannan magana ba ta da tushe.

Ya jinjina wa Tinubu bisa jajircewarsa da ƙwarewarsa wajen bunƙasa siyasa, saɓanin El-Rufai da ya ce mutum ne da ke canza jam’iyya akai-akai don son zuciya.

Ata, ya tabbatarwa da ’yan Najeriya cewa APC na ƙoƙarin ci gaba da gina ƙasa, inda ya buƙace su da kada su saurari kalaman El-Rufai.

Ya ce gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da aiki tuƙuru wajen bunƙasa tattalin arziƙi, bunƙasa ababen more rayuwa da tabbatar da tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A Legas  Ya Koma APC Daga PDP
  • Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci
  • Nijar ta kori wasu kamfanonin China 3 daga ƙasar
  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  • Minista ya caccaki El-Rufai kan sukar Tinubu da APC
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 
  • ’Yan Adawa Na Kitsa Makarkashiyar Tsige Ni – Akpabio
  • MDD : Kwamitin Sulhu ya yi tir da kisan kiyashin Siriya