Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a Adamawa
Published: 17th, March 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Adamawa ta cafke wani ƙani da yayansa — Aliyu Abdulmalik da Ibrahim Abdulmalik — kan zargin yanke kan wani almajiri ɗan shekara 10, Abdallah Lawali.
Bayanai sun ce ’yan uwan junan biyu sun aikata wannan ta’asa ce a ranar 7 ga watan Maris a unguwar Sarkin Yamma da ke Ƙaramar Hukumar Jada.
Sanarwar da rundunar ’yan sandan ta fitar ta ce an kama ababen zargin ne da gangar jikin almajirin a cikin wani buhu, yayin da aka ƙwaƙulo kansa a cikin wani rami da suka binne a harabar gidansu.
Rundunar wadda ta ce yanzu haka bincike ya kankama a kan lamarin, ta kuma bayyana cewa ababen zargin sun yi iƙirarin aikata laifin da suka alaƙanta da sharrin shaiɗan.
Kwamishinan ’yan sandan jihar CP Dankombo Morris, ya tabbatar da cewa za a yi adalci a lamarin, yayin da yake kira ga al’umma da su kasance masu lura da miƙa rahoton duk wani motsi da su aminta da shi ba zuwa ofishin mahukunta mafi kusa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Adamawa Wa da ƙani
এছাড়াও পড়ুন:
Amnesty Ta Zargi Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ” Amnesty International” ta bayyana cewa, rundunar kai daukin gaggawa ta “RSF” ta bautar da mata da kuma cin zarafinsu.
Kungiyar ta yi tir da abinda rundunar ta “RSF” ta yi akan mata da su ka manyanta da kuma ‘yan mata a tsawon lokacin yakin na Sudan da har yanzu bai zo karshe ba.
Wani sashe na rahoton kungiyar ya yi ishara da yadda wannan rundunar da take fada da sojojin kasar Sudan ta tarwatsa mutane daga gidaje da matsugunansu a fadin kasar.
Ita kuwa Hukumar dake kula da ‘yan gudun hijira ta MDD ( UNHCR) cewa ta yi da akwai yan kasar ta Sudan fiye da 100,000 da suke neman yin hijira zuwa kasashen turai a cikin wannan shekara ta 2025 kadai, tare da kara da cewa mutanen suna kara yanke kauna da samun wata mafita a cikin kasar, saboda raguwar agaji.
A cikin birnin Khartum da sojojin su ka kori dakarun na “RSF” an sami komawar mutanen da su ka yi hijira kamar yadda hukumar ta ( UNHCR) ta ambata.
Shugabar hukumar mai kula da ‘yan hijira ta MDD Olga Sarado wace ta gudanar da taron manema labaru a birnin Geneva ta bayyana cewa; Da akwai ‘yan Sudan su 484 da su ka isa cikin kasashen turai daga watan Janairu zuwa yanzu, da hakan yake nuni da samun Karin masu hijirar zuwa turai da kaso38%.
Ta kuma kara da cewa, matukar ba a kai wa kasar kayan agaji, to kuma masu yin hijira zuwa turai din zai karu.