HausaTv:
2025-03-17@22:50:57 GMT

MDD ta bukaci masu ruwa da tsaki a Yemen da su kai zuciya nesa

Published: 17th, March 2025 GMT

Babban sakantaren MDD António Guterres, ya yi kira ga mabambantan bangarori masu ruwa da tsaki a Yemen da su yi iyakacin kokarin yin hakuri da juna, su kuma dakatar da kowane irin matakin soja, inji kakakinsa a wata sanarwa.

Sanarwar ta ce, “Mun lura da cewa, Amurka ta kai hare-hare da dama kan wasu wurare dake karkashin ikon ‘dakarun’yan Houthi, lamarin da ya haddasa asarar rayuka da dama.

Sanarwar ta kara da cewa, “Kowane matakin soja da za a dauka na iya tsananta halin da ake ciki, zai kuma haifar da mummunan tasiri, tare da gurgunta yanayin kwanciyar hankali a Yemen, kana zai kara kamarin kalubalen halin jin kai a kasar.”

‘Yan Houthi dai sun yi barazanar karin kai hare-hare kan jiragen ruwa dake ratsa tekun maliya”.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Soja ya shafe mako guda da harsashi a cikin ƙwaƙwalwarsa

Kafofin yada labaran kasar Rasha sun yi ta jinjina wa wani sojan kasar a matsayin jarumi saboda ci gaba da fafatawa a yankin Kursk tsawon mako guda bayan harbin da aka yi masa a ka.

Mutumin da ba a bayyana sunansa ba, wanda aka ruwaito cewa yana cikin Brigade na 155 na Marine na Rukunin Pacific Fleet na Rasha, ya ci gaba fafatawa da sojojin Ukraine a Kursk lokacin da aka harbe shi.

Nijar ta kori wasu kamfanonin China 3 daga ƙasar Faɗuwar farashin kayan abinci a watan azumi ta shammace mu – ‘Yan kasuwa

A lokacin an harbi hular kansa, amma yana tunanin tabbas harsashin ya huda cikinta.

Ya samu kumburi a saman idonsa, wanda daga ƙarshe ya sa idonsa ya fara rufewa, amma sai kawai ya ci gaba da harkokinsa, yana tunanin kumburin zai warke da kansa.

Sai dai bayan wani rauni da ya samu mai alaka da rauni ne ya sa sojan ya ziyarci asibiti, inda ya samu labarin cewa harsashin da ya soki kwakwarsa ya huda kokon kansa ya shiga kwakwalwarsa.

Hotunan sojan sun nuna ya samu mummunan rauni a wani wuri da harsashi ya ragargaza hularsa, inda gefan idonsa daya ya kumbura, amma ba a san yadda shi ko sauran sojojin suka gano raunin harsashin ba.

An yi zargin cewa mutumin ya ci gaba da fafatawa a fagen daga har tsawon mako guda ba tare da wata matsala ba, illa kumburin gefan idonsa.

Sai bayan da likitocin Rasha suka ɗauki hoton wurin sannan suka gano wani babban harsashin bindiga maƙale a ƙwaƙwalwar sojan.

Sun kalli lamarinsa a matsayin abin al’ajabi da ba kasafai yake faruwa ba, kuma a yanzu ana yaba wa mutumin saboda juriyarsa.

Wasu ma suna kira ga sojojin Rasha da su karrama shi da lambar yabo.

Wannan labari da ba a saba gani ba ya tuno da wani labari na yaƙi mai ban mamaki, inda sojan yaƙin basasar Amurka, Jacob Miller, wanda ya rayu tsawon shekara 50 bayan an harbe shi a goshi inda aka yi masa aiki a kwakwalwarsa.

Hotunansa da wani rami da ake gani a goshinsa na ta yaɗuwa a shafukan sada zumunta a yau.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Yemen sun sha alwashin tsayin-daka kan barazanar Trump
  • Yemen: Amurka Ta Sake Kai Wani Harin A Kasar Yemen
  • Kungiyar Ansarullah Ta Ce Keta Hurumin Kasar Da Amurka Ta Yi Zai Gamu Da Maida Martani
  • Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen
  • Fiye Da Mutane 20 Ne Su Ka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren  Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
  • Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi
  • Kungiyoyin Falasdinawa Suna  Cigaba Da Yin Allawadai Da Hare-haren Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
  • Soja ya shafe mako guda da harsashi a cikin ƙwaƙwalwarsa
  • NPA Za Ta Yunkuro Don Zamanantar Da Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya – Dantsoho