Ofishin kwamitin kolin JKS da na majalisar gudanarwar kasar Sin, sun sanar da kaddamar da sabon shiri game da tsare-tsaren musamman na bunkasa sayayya a kasar Sin, a gabar da kasar wadda ita ce ta biyu a karfin tattalin arziki a duniya ke kara karkata ga mayar da kasuwannin gida ginshiki, kuma babban karfi na ingiza ci gaban tattalin arzikinta.

Shirin wanda ofisoshin biyu suka yi hadakar sanar da shi a jiya Lahadi, ya kunshi dabarun bunkasa sayayya, da ingiza bukatun cikin gida a dukkanin sassa, da fadada karfin sayayya ta hanyar kara yawan kudaden shiga, da rage nauyin da al’umma ke fuskanta ta fuskar bukatun kudi.

Kazalika, shirin na fatan ingiza karin bukatu ta hanyar samar da ingantattun hidimomin gabatar da hajoji, da kara kyautata muhallin sayayya ta hanyar karfafa gwiwar al’umma don yin sayayya, da magance kalubale dake yiwa al’umma tarnaki wajen sayayya.

Bugu da kari, shirin wanda aka tsara zuwa manyan sassa 8, zai mamaye dukkanin sassa ta hanyar magance mataloli, kamar wadanda ke dakile karuwar kudaden shiga, da masu tarnaki ga ingancin hidimomi, da daga matsayin sayayyar abubuwa da ake mallaka ta manyan tikiti, da kara inganta yanayin muhallin sayayya. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yunkurin Neman ‘Yancin Kan Taiwan Ya Shaida Yunkurin Lai Ching-te Na Neman Mulki Irin Na Kama Karya Ta Hanyar Demokuradiyya

Kalmar demokuradiyya kalma ce da jagoran ‘yan awaren Taiwan Lai Ching-te ke yawan ambata, amma aikin da ya yi bai bi hanyar demokuradiyya ba. A baya-bayan nan, Lai Ching-te ya gabatar da wani shirin neman ‘yancin kan Taiwan, har ma ya ce wai Taiwan wata kasar demokuradiyya ce mai mulkin kanta. Lai Ching-te ya kan yin amfani da demokuradiyya don ya cuci jama’ar yankin Taiwan da sauran kasashen duniya, amma a wannan karo kowa ya san yunkurinsa na neman mulki irin na kama karya ta hanyar demokuradiyya.

Ya kamata a yi amfani da demokuradiyya don tabbatar da hakkin jama’a, a maimakon kawo illa ga hakkin jama’a. Jama’ar yankin Taiwan suna neman zaman lafiya, da samun ci gaba, da yin mu’amala, da kuma yin hadin gwiwa. Bisa binciken shekara kan huldar dake tsakanin bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan da kafofin watsa labaru na yankin Taiwan suka bayar a shekarar 2024, kashi 87 cikin dari na jama’ar yankin Taiwan sun yi tsammanin cewa, akwai bukatar kiyaye yin mu’amala a tsakanin bangarorin biyu na mashigin tekun Taiwan. Amma tun lokacin da mahukuntan jagoran ‘yan awaren Taiwan Lai Ching-te suka kama aiki a watan Mayu na shekarar bara, sun yi amfani da hanyoyin ayyukan gwamnati da dokoki da kafofin watsa labaru don hana yin mu’amala a tsakanin bangarorin biyu na mashigin tekun Taiwan.

Mahukuntan Lai Ching-te sun yi aika-aikar da ta janyo koma baya a tarihi da keta ‘yanci da hakkin dan Adam na jama’ar yankin Taiwan, kana tana son shigar da jama’ar cikin ayyukan ‘yan awaren Taiwan, da bayyana cewa wai yankin Taiwan muhimmin yanki ne da ke tabbatar da demokuradiyya a duniya. Yunkurinsa na neman ‘yancin kan Taiwan wanda ya keta bukatun jama’a da demokuradiyya ba zai samu nasara a tarihi ba. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kokarin Kasar Sin Na Bunkasa Hadin Gwiwar Neman Ci Gaban Duniya Na Nan Daram
  • Maggi Ya Kaddamar Da Wasanni Na Musamman Domin Watan Ramadan
  • Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano
  • Ko Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Laliga Ta Bana?
  • Kasar Habasha Ta Bukaci Kasashen Afirka Su Bunkasa Ciyar Yaki Da Cututtuka CDC Da Kungiyar
  • Yunkurin Neman ‘Yancin Kan Taiwan Ya Shaida Yunkurin Lai Ching-te Na Neman Mulki Irin Na Kama Karya Ta Hanyar Demokuradiyya
  • Ramadan Iftar: Sarkin Kauru Ya Hori Al’umma Su Hada Kai Su Zauna Lafiya da Juna
  • An Cafke Wadanda Ake Zargi Da Daba Wa Dan Wasan Nijeriya Mazaunin Kasar Ireland Wuka Har Lahira
  • Tsohon Firaministan Lebanon: Rashin Fahimta Da Shakku Daga Waje Ba Za Su Iya Dakatar Da Ci Gaban Kasar Sin Ba