Maggi Ya Kaddamar Da Wasanni Na Musamman Domin Watan Ramadan
Published: 17th, March 2025 GMT
Wasan na tare da jarumai da suka hada da Rekiate Ibrahim-AttahRekiya Attah, Ramadan Booth, Rabiu Rikadawa, da sauran jarumai. ‘MAGGI Tales of Ramadan’ yana kunshe da darussa masu kayatarwa da aka tsara na mako 6 wanda zai fara daga farkon watan Ramadan. A yayin kallon wasan za a fuskanci muhimman abin da zai karfafa soyayya a tsakanin al’umma.
A kowanne shafi na labarin zai fito da cikakken abubuwan da suke tattare da darussan watan Ramadan a tsakanin al’umma gaba daya musamman ganin yadda aka kama baki da rana har aka zo yin buda baki da kuma lokacin da yin sahur.
A jawabinta, shugabar vangaren kula da sarrafa MaGGI na kamfanin Nestlé Nigeria, Mrs Rahamatou Palm-Zakari ta bayyana cewa, “Ramadan lokaci ne na rarraba abin da aka mallaka cikin jin dadi da annashuwa a tsakanain al’umma, kuma mun fara wannan taarin ne fiye da shekara goma da suka wuce. Za kuma mu ci gaba da tallafa wa iyalai a cikin al’umma kamar yadda muka saba a baya
Mun kuma yi alkawarin tattaro mutane daga sassan kasa wuri daya, tabbas MAGGI ya yi imanin zaburar da mtane donm su nuna soyayya a tsakanin su musamman wanna lokaci na Ramadan.
MAGGI na daga cikin abubnwan alfarma da kamfanin Nestlé ke sarrafawa. Muna kuma alfahari da cewa al’umma dama har ma da wadanda ba a haifa yanzu za su ci gaba da amfana da shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
A daidai lokacin da ake ci gaba da takaddama a HKI dangane da wasikar da wasu sojojin sama su ka rubuta na sukar yakin Gaza, wasu tsoffin ma’aikatar hukumar leken asiri ta “Mosad” sun bi sawunhu.
Kafafen watsa labarum HKI sun ambaci cewa, fiye da tsoffin jami’an leken asirin kungiyar MOSAD 200 ne su ka rattaba hannu akan wata takarda suna nuna goyon bayansu da sojan sama da su ka yi kira a kawo karshen yakin Gaza.
Kwanaki kadan da su ka gabata, tashar talabijin din Channel 13; ta watsa labarin da yake cewa; Wasu ma’aikatar rundunar leken asiri ta soja sun shiga cikin masu kira da a kawo karshen yakin na Gaza da kuma dawo da fursunoni daga can.
An kuma samu irin wannan halayyar ta yin kira a kawo karshen yakin a tsakanin likitocin soja su 100 sai kuma malaman jami’a su ma daruruwa.
Kiraye-kirayen da sojojii suke yi a HKI da na kwo karshen yakin Gaza da mayar da fursunonin yaki, ya bude wata sabuwar takaddama a tsakanin ‘yan siyasa.
Wasikar ta bude jayayya a tsakanin ‘yan sahayoniya akan cewa, Netanyahu yana ci gaba da yin yaki ne saboda maslahar kashin kansa.