“Dole ne mu ci gaba da bunkasa jiharmu, kuma an gina wadannan gidajen ne don habaka jiharmu.

 

“Ga dukkan masu gidaje da ke wadannan jerin gidaje, ina sanar da su a fili, ko dai su koma wuraren da zama ko kuma a kwace,” in ji Gwamna Yusuf.

 

Ya kuma bukaci wadanda ba za su iya komawa wuraren ba da su yi tunanin yiwuwar bayar da hayar gidajensu, yana mai jaddada kudirin gwamnati na ganin wuraren sun ci gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano

Gwamna Abba Kabir Yusuf a wannan Litinin ɗin ya rantsar da sabon Kwamishinan Ma’aikatar Tsarawa da Bunƙasa Gidaje ta Kano, Ibrahim Yakubu Adamu.

Wannan dai shi ne karo na huɗu cikin ƙasa da shekaru biyu ke nan da gwamnan yake faɗaɗa majalisar zartarwa jihar ta Kano.

Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a Adamawa Majalisar Ribas ta soma shirye-shiryen tsige Gwamna Fubara

Aminiya ta ruwaito cewa gabanin wannan sabon naɗin, Ibrahim Yakubu Adamu shi ne Shugaban Hukumar Tsara Birane ta Kano KNUPDA.

Antoni Janar kuma Kwamishinan Shari’a na Kano, Haruna Isah Dederi ne ya jagoranci rantsar da sabon Kwamishinan da aka gudanar a fadar Gwamnatin Kano.

Da yake jawabi, Gwamnan ya yaba wa sabon kwamishinan wanda ya ba da shaida kan ƙwazo da kuma ƙwarewa haɗi da gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban birnin na Dabo.

Gwamnan ya buga misali da yadda sabon kwamishinan ya jagoranci aikin tsarawa da kuma bunƙasa rukunin gidajen nan na Kwankwasiyya da Amana da Bandirawo waɗanda aka gina a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015 a zamanin gwamnatin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Sabon kwamshinan wanda ƙwararren mai zana gine-gine ne, Gwamnan ya hikaito yadda ya taka rawar gani wajen tsarawa da kuma aiwatar da wasu muhimman ayyukan gine-gine a lokacin da yake Kwamishinan Ayyuka da Gidaje a tsakanin shekarar 2011 zuwa 2015.

A wani labarin mai nasaba da wannan, Gwamnan ya umarci duk waɗanda suka mallaki gida a rukunin gidaje na Kwankwasiyya ko Amana ko Bandirawo da su tabbatar sun tare nan da watanni uku ko kuma su sanya ’yan haya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MOFA: Ya Kamata G7 Ya Mai Da Hankali Kan Habaka Hadin Kai Da Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa 
  • Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano
  • Al’ummar Yemen sun sha alwashin tsayin-daka kan barazanar Trump
  • Ba Don Tarbiyantar Da Mutane Nake Yin Fim Ba -Amina Shehu Lulu
  • Darajar Kasuwar Kayan Aikin Likitancin Kasar Sin Ta Kai Yuan Triliyan 1.35
  • Ma’aikatar Ilimin Amurka Na Shirin Korar Ma’aikata 1,300
  • Malaman Da Aka Dakatar 207, Sun Mika Takardar Neman Afuwa Ga Gwamnatin Zamfara
  • Gwamnatin Trump na tunanin hana ‘yan kasashe kusan 40 ciki har da Iran shiga Amurka
  • Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan