Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; Dukkanin batutuwan  da Musulunci da kuma al’kur’ani maigirma suke bijiro da su, sun ginu ne akan ginshikin gaskiya da kuma adalci.

Shugaban kasar ta Iran ya kara da cewa; Idan har wadannan ginshikan biyu su ka zama ana aiki da su a cikin al’umma, to za a sami shiriya.

Shugaba Mas’ud Fizishkiyan ya kuma ce; A wannan lokacin muna da bukatuwa da koyar da dalibai da ‘ya’yanmu domin su kai ga mataki na koli na ilimi da kuma kyawawan halaye, ta yadda za su zama karfin madogara da hikima da kyawawan halaye a cikin al’umma.

Shugaban na kasar Iran ya kuma ce: Abubuwan da musulunci da kuma al’kur’ani suke bijiro da su, sun ginu ne akan ginshikai biyu da su ne  gaskiya da kuma adalci a cikin dukkanin fagage.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Amurka Ya Kara Yawan Kasashen Da Ya Sa Wa Takunkumin Shiga Amurka

Shugaban kasar ta Amurka Donald Ttump ya kara yawan kasashen da ya sa wa takunkumin shiga cikin Amurka zuwa kasashe 43.

Daga cikin kasashen da ya sa wa sharuddan shiga cikin kasar Amurka sun hada guda 11 da su ne; Somaliya, Sudan, da Libya. Sai kuma Afghanistan, Cuba, Iran, Korea Ta Arewa, Syria, Venezuela da kuma Yemen.

A lokacin zangonsa na farko Trump matakin nasa ya ja hankalin duniya saboda yadda ya hana ‘yan hijira daga kasashen Iraki,  Libya, Somaliya, Sudan da Yemen shiga cikin kasar.

An kalubalanci matakin na shugaban kasar Amurka a wancan lokacin a kotu saboda yadda ya shafi mafi yawancin kasashen musulmi.

Bayan da Joe Biden ya zama shugaban kasa ya soke wancan matakin na Donald Trump a 2021.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Putin Na Kasar Rasha Zai Zanta Ta Wayar Tarho Da Tokwaransa Na Kasar Amurka Donal Trump
  • Mayakan “Jubhatun-Nusrah’ Na Kasar Syria Sun Kai Hari Akan Iyakar Kasar Leabnon
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Kara Yawan Kasashen Da Ya Sa Wa Takunkumin Shiga Amurka
  • Baka’i: Za Mu Mayar Da Martani Akan Wasikar Trump Bayan Yin Nazari
  • Iran Ta Yaba Da Yarjeniyar  Zaman Lafiya Da Aka Cimma Tsakanin Kasashen Armenia Da Azerbaijan
  • Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci
  • Kofar JMI A Bude Take Don Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi
  • Kungiyoyin Falasdinawa Suna  Cigaba Da Yin Allawadai Da Hare-haren Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen