Rwanda Ta Yanke Huladar Diflomasiyya Da Kasar Belgium
Published: 18th, March 2025 GMT
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Rwanda ya fitar, ta zargi kasar ta Belgium da tsoma baki a harkokin cikin gidanta.
Bugu da kari, sanarwar ta bai wa jakadan kasar Belgium a Kigali sa’o’i 48 da ya fice ya bar kasar.
Sanarwar ta kunshi cewa: A kodayaushe kasar Belgium tana kaskantar da Rwanda,tun kafin rikicin kasar DRC, da kuma bayansa, alhali kasar ta Belgium tana da dogon tarihi ta keta, musamman akan Rwanda.
Kasar Belgium dai ta dakatar da taimakon da take bai wa Rwanda saboda rawar da Kigali take takawa a rikicin kasar DRC.
A wani jawabi da shugaban kasar ta Rwanda ya yi a ranar Lahadi ya bayyana cewa; Kasarsa za ta kare manufofinta da hana kasashen waje yi ma ta katsalandan a harkokin cikin gidanta. Haka nan kuma ya zargi Belgium din da aikata laifuka a tsawon lokacin mulkin mallakar da ta yi wa kasarsa, yana mai kara da cewa za su ci gaba da fada da sabon salon mulkin mallaka.
Kasar ta Rwanda tana fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya saboda goyon bayan da take bai wa ‘yan tawayen kungiyar M23 da su ka kwace iko da manyan biranen Bukavu da Goma da suke a gabashin kasar DRC. Ana zargin cewa kasar ta Rwanda ta aike da sojoji 4000 da suke yaki a tare da ‘yan tawayen.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Belgium
এছাড়াও পড়ুন:
Netanytahu Ya Fusta Da Furucin Kasar Canada Akan Kisan Kiyashi A Gaza
Fira ministan HKI Benjamine Netanyahu ya yi suka cikin fushi saboda Fira ministan kasar Mark Carney Canada ya bayyana cewa abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne.
Shi dai Fira ministan kasar Canada Mark Carney wanda ya halarci taron yankin neman zabe a garin Calgary, yayin da wani daga cikin mahalarta, ya daga murya da karfi yana fada wa Fira ministan cewa, Abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne. Shi kuwa Mark Carney ya amsa mas ada cewa; Ina da masaniya, kuma shi ne dalilin da ya sa kasar Canada ta daina sayar wa da Isra’ila makamai.
Sai dai kuma kwana daya bayan abinda ya faru, fira ministan na kasar Canada ya lashe amansa inda ya bayyana cewa, bai ji kamlar kisan kiyashi ba, a cikin abinda aka ambata.
Wannan bai hana Fira ministan na HKI sukar takwaransa na Canada ba,tare da bayyana shi a matsayin mai kin jinin yuhudawa.
Su kuwa kungiyoyin kare hakkin bil’adama na cikin kasar Canada sun bayyana ja da bayan da Fira minstan ya yi da cewa, ba abinda za a laminta da shi ba ne, ya zama wajibi a gare shi da ya goyi bayan MDD da kungiyoyin kasa da kasa na kare hakkin bil’adama akan cewa; Abinda yake faruwa a Falasdinu kisan kiyashi ne.
Alaka a tsakanin HKI da kuma kasar Canada suna kara kamari,a lokacin da kungiyoyin kasa da kasa suke kara yi wa Tel Aviv matsin lamba akan kawo karshen yakin da take yi a Gaza.