Trump Zai Tattauna Da Putin Kan Kawo Ƙarshen Yaƙin Ukraine
Published: 18th, March 2025 GMT
A ranar Juma’a, fadar Kremlin ta ce Shugaba Putin ya aike saƙo zuwa ga Trump ta hannun manzon Amurka na musamman, Steve Witkoff, yana bayyana cewa Rasha tana nazarin batun tsagaita wuta amma tana taka-tsantsan.
Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya ce yana fatan wannan tattaunawa za ta kai ga samun mafita, amma ya jaddada cewa dole ne Rasha ta mayar da yankunan da ta ƙwace.
Tun a shekarar 2014, Rasha ta ƙwace yankin Crimea, sannan a shekarar 2022 ta mamaye wasu yankuna huɗu na gabashin Ukraine.
Yanzu dai ana fatan wannan tattaunawa za ta kawo ƙarshen rikicin da ya daɗe yana ci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Rasha Tattaunawa Ukraine
এছাড়াও পড়ুন:
Rwanda Ta Yanke Huladar Diflomasiyya Da Kasar Belgium
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Rwanda ya fitar, ta zargi kasar ta Belgium da tsoma baki a harkokin cikin gidanta.
Bugu da kari, sanarwar ta bai wa jakadan kasar Belgium a Kigali sa’o’i 48 da ya fice ya bar kasar.
Sanarwar ta kunshi cewa: A kodayaushe kasar Belgium tana kaskantar da Rwanda,tun kafin rikicin kasar DRC, da kuma bayansa, alhali kasar ta Belgium tana da dogon tarihi ta keta, musamman akan Rwanda.”
Kasar Belgium dai ta dakatar da taimakon da take bai wa Rwanda saboda rawar da Kigali take takawa a rikicin kasar DRC.
A wani jawabi da shugaban kasar ta Rwanda ya yi a ranar Lahadi ya bayyana cewa; Kasarsa za ta kare manufofinta da hana kasashen waje yi ma ta katsalandan a harkokin cikin gidanta. Haka nan kuma ya zargi Belgium din da aikata laifuka a tsawon lokacin mulkin mallakar da ta yi wa kasarsa, yana mai kara da cewa za su ci gaba da fada da sabon salon mulkin mallaka.
Kasar ta Rwanda tana fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya saboda goyon bayan da take bai wa ‘yan tawayen kungiyar M23 da su ka kwace iko da manyan biranen Bukavu da Goma da suke a gabashin kasar DRC. Ana zargin cewa kasar ta Rwanda ta aike da sojoji 4000 da suke yaki a tare da ‘yan tawayen.