Wata 11 da tuɓe rawanin wasu sarakuna a Sakkwato
Published: 18th, March 2025 GMT
An shiga wata 11 da Gwamnatin Jihar Sakkwato ƙarƙashin Gwamna Ahmad Aliyu ta tuɓe rawanin wasu sarakuna da take ganin sun yi abin da bai dace ba na shiga siyasa.
Tun bayan cire sarakunan, mutane sun yi tsammanin gwamnati za ta nada wadanda take muradi ne kai-tsaye domin su maye gurbin tubabbun sarakunan, amma shiru kamar ba wasu da ke jiran hukunci da sakayyar gwamnati mai ci.
Har yanzu gwamnati ba ta fito ta fadi dalilin rashin sake nada sababbin sarakunan ba domin ci gaba da wakilcin jama’a, ganin an bar garin kufai ba cikakken basarake.
A baya da ma sarukanan da aka tube sun jima suna dakon sakamakon bincikensu da gwamnatin ke yi, sai dai wasu jama’a musamman na ɓangaren jam’iyyar adawa na ganin bita da ƙulli ne gwamnatin ta yi musu.
Kakakin Gwamnatin Jihar Sakkwato, Abubakar Bawa ya ce, wadanda aka sauke daga mukamansu sun hada da iyayen kasar Unguwar Lalle da Yabo da Wamakko da Tulluwa da Illela da Dogon Daji, da Kebbe da Alkammu da Tambuwal da na Giyawa, a kananan hukumomi 10 na jihar.
Haka kuma an tube wasu iyayen kasa shida bisa dalilin cewa lokacin da aka nada su, an yi gaggawa ba a bi ka’ida ba.
Sai kuma wasu biyu da aka sauya wa wurin aiki, wadanda daya daga cikinsu ‘dan majalisar Sarkin Musulmi ne da sabon Magajin Gari da aka mayar masa sarautarsa ta da, yayin da za a ci gaba da gudanar da bincike a kan wasu iyayen kasar hudu.
Har ila yau, an amince da wasu iyayen ƙasa tara daga cikin wadanda aka bincika a kan su ci gaba da aikinsu.
To sai dai wasu jama’ar jiha musamman na ɓangaren jam’iyar adawa ta PDP na ganin wannan bai zo da mamaki ba domin da ma a cewarsu wannan gwamnatin ta ƙudiri aniyar cin zarafin sarakuna iyayen al’umma.
Hassan Sahabi Sanyinnawal kakakin jam’iyar ta adawa ce inda ya ce, rashin sanin aiki ne gwamnati ta ce, an naɗa wasu sarakuna ba bisa ka’ida ba.
Amma shi kuwa kakakin Gwamnatin Jihar Sakkwato kuma kakakin Jam’iyar APC mai mulki, Sambo Bello Danchadi ya ce, abin da gwamnati ta yi a kan ka’ida yake.
Jama’a da dama sun tofa albarkacin bakinsu a kan wannan lamarin, inda wasu suke ganin an yi daidai, duba da dalilan da aka bayar na tube sarakunan wasu kuma na ganin akasin haka, yayin da sauran iyayen kasa hudu da ake ci gaba da bincike a kansu ke dakon jiran sakamako.
An jima dai ana zargin sarakuna da tsoma hannu ga lamuran siyasa a Nijeriya, abin da kuma wasu lokuta yakan zo musu da mummunan sakamako.
Gaba dyaya gwamnati ta fita batun wannan lamari wanda ake ganin akwai buƙatar a tuna wa gwamnati domin lamari ne mai girma a wannan lokaci na matsalar tsaro, a ƙyale wasu jama’a ba cikakken sarki da ke kula da shige ficensu a yankinsu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A Legas Ya Koma APC Daga PDP
Tsohon ɗan takarar gwamna a jihar Legas na jam’iyyar PDP, Dr. Olajide Adediran, wanda aka fi sani da Jandor, ya sanar da koma wa jam’iyyar APC mai mulki. Wannan sanarwar ta zo ne bayan kwanaki biyu kacal da ya fice daga jam’iyyar PDP.
Jandor ya ba da sanarwar koma wa jam’iyyar APC ne a wani taron manema labarai da aka gudanar a ofishin yaƙin neman zaɓensa da ke Ikeja a ranar Litinin. Ya bayyana cewa ya yi shawarwari da shugaban ƙasa Bola Tinubu, tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, da wasu manyan mutane a fagen siyasa bayan ya fice daga PDP.
El-Rufai Ya Yi Alƙawarin Haɗa Abokan Hamayya Don Yaƙar APC A Zaɓen 2027 Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – AtikuKakakin Jandor, Gbenga Ogunleye, ya tabbatar da cewa taron da ya yi da shugaban ƙasa ya gudana ne a ranar Litinin da ya gabata. Ya kuma bayyana cewa Jandor ya gana da wasu manyan shugabanni kamar tsohon shugaban ƙasa Ibrahim Babangida, tsohon shugaban mulkin soja Abdusalami Abubakar, da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar SDP a zaben 2023, Prince Adewole Adebayo, domin yin shawarwari kan matakin da ya ɗauka.
Haka kuma, sakataren jam’iyyar PDP na ƙasa da wasu shugabannin jam’iyyar sun ziyarce shi kwanan nan domin roƙonsa ya dakata kan matakin ficewa daga jam’iyyar. Duk da haka, Jandor ya ƙuduri aniyar ci gaba da shirye-shiryensa na siyasa a cikin jam’iyyar APC.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp