Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujeru 54 na Hajj ga malamai da jami’an da za su jagoranci Alhazai don aikin Hajjin 2025.

Babban Daraktan hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga wakilin Radio Nigeria a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujerun ne domin bai wa jami’ai  da malamai damar jagorantar Alhzan jihar a Najeriya da Saudiyya.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, wannan tsari da hukumar ta kirkiro shi ne irinsa na farko a tarihin Jihar Jigawa.

 

Ya bayyana cewa, an zabi jami’an da malamai maza da mata daga  daga kananan hukumomi 27 na jihar bisa cancanta.

Ya jaddada cewa, an zaɓi mutum biyu daga kowace karamar hukuma ta jihar.

Babban Daraktan ya bayyana cewa,  malamai da jami’an sun samu umarni don koyar da maniyyata game da wajiban Hajj, ka’idoji da kuma manyan ginshiƙan aikin Hajj domin su san yadda za su gudanar da ibadar Hajj yadda ya kamata.

 

Ya bayyana cewa, bayar da cikakken horo da ilimantar da maniyyata zai taimaka musu wajen gudanar da Hajj bisa koyarwar addinin Musulunci tare da wakiltar Najeriya da kyau.

Ya ƙara da cewa, za a ci gaba da gudanar da bita ga maniyyatan Hajj na 2025 a dukkan cibiyoyin da aka kebe bayan Ramadan.

Ahmed Labbo ya ce, hukumar za ta fara raba kayayyakin tafiya ga maniyyatan Hajj na 2025 nan ba da daɗewa ba.

A cewarsa, rarraba kayayyakin tafiya wadanda suka  haɗa da yunifom da jakunkuna zai fara nan gaba a hedkwatar hukumar da wasu cibiyoyi da aka ware a faɗin kananan hukumomi 27 na jihar.

Ya bayyana cewa, jirgin farko na jigilar maniyyatan jihar zai tashi a  watan Mayu 2025 kamar yadda Hukumar Hajj ta Kasa (NAHCON) ta tsara.

Labbo ya jaddada cewa, NAHCON ta ba Max Air damar jigilar maniyyatan jihar zuwa Saudiyya ta filin jirgin sama na Nuhu Muhammadu Sunusi International Airport.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan ya gode wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.

 

USMAN MUHAMMAD ZARIA 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Ya bayyana cewa ya bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kofin Duniya: ’Yan wasan cikin gida 8 da Super Eagles ta gayyata

Tawagar Kwallon Kafa ta Super Eagles ta Nijeriya ta gayyaci sababbin ’yan kwallo takwas da za su wakilci kasar domin buga mata wasannin neman gurbin shiga Gasar Kofin Duniya na 2026.

Tuni Super Eagles karkashin jagorancin sabon mai horaswa Eric Chelle, ta fitar da jadawalin ’yan wasa na farko da za su taka mata leda a wasannin neman gurbin da za ta take a watan Maris din nan da muke ciki.

NAJERIYA A YAU: Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan Isra’ila ta ƙaddamar da sabon hari a Zirin Gaza

Daga cikin sababbin ’yan wasan da ta gayyato da ba su taba wakiltar Nijeriya ba, har da irin su Papa Mustapha da Ifeanyi Emmanuel Onyebuchi da Christantus Uche da Akor Adams da Tolu Arokodare da Igoh Ogbu da Anthony Dennis da Kayode Bankole.

A ranar 26 ga watan Maris ɗin nan Super Eagles za ta je birnin Kigali domin fafatawa da tawagar ’yan wasan ƙasar Rwanda.

Ranar 25 kuma za ta goge raini tsakanin ta da Zimbabwe a nan gida Nijeriya a Filin Wasa na Godswill Akpabio da ke garin Uyo, Jihar Akwa Ibom.

Eric ya gayyato Ahmed Musa

Abin da ya ɗauki hankalin mutane a jerin ’yan wasan da Super Eagles ta fitar shi ne yadda a wannan lokacin ta gayyato ’yan wasan da suke taka leda a gasar Firimiya ta cikin gida su wakilci kasar.

Cikin ’yan wasa na cikin gidan har da tsohon Kyaftin din tawagar, Ahmad Musa, wanda tun bayan komawarsa Kungiyar Kwallon Kafa ta Kano Pillars a farkon shekarar 2024, bai sake samun gayyata daga Super Eagles ba sai wannan karon.

Papa: Daga cikin ’yan wasan da aka gayyato a nan gida Nijeriya akwai irinsu Papa Mustapha Daniel, dan wasan tsakiya da ke taka leda a Kungiyar Niger Tornados da ke birnin Minna na Jihar Neja.

Matashin mai shekara 23 dan Jihar Legas, kuma ya koma taka leda ne a kungiyar Niger Tornados a watan Agustan shekarar 2024.

Kafin ya koma Niger Tornados, ya taka leda a Kungiyar Adanaspor da kasar Turkiyya, sannan ya wakilci tawagar ’yan Najeriya masu taka leda a cikin gida.

Onyebuchi: Sai kuma Emmanuel Onyebuchi dan wasan baya da yake taka leda a Kungiyar Rangers International FC da ke Jihar Enugu.

Matashin dan wasan mai shekara 24 mazaunin Jihar Kaduna ne, inda ya fara buga kwallo.

Ya kuma taka leda a kungiyoyin Plateau United da MFM FC da FC Shkupi da ke kasar Macedonia ta Arewa kafin ya koma Rangers.

Bankole: Akwai kuma Kayode Bankole na Remo Stars, mai shekaru 22, wanda matashin mai tsaron gida ne da ke tashe a Gasar Firimiya ta Nijeriya.

Matashin golan ya fara tsaron gidan Kungiyar Remo ne a kakar shekarar 2020. Kafin nan ya tsare ragar Kungiyar Shooting Stars a kakar 2019 zuwa 2020.

Kayode Bankole haifaffen garin Ipokia ne da ke Jihar Ogun.

Ahmed Musa: Sai kuma wanda aka fi mayar da hankali a kansa, Ahmed Musa, wanda Kyaftin ne na tawagar ta Super Eagles, amma ya dade ba ta gayyace shi ba, lamarin da ake tunanin ko dai don ya koma Firimiyar Nijeriya ne da taka leda.

Tsawon lokaci an yi ta jiran ganin ko sabon kocin Super Eagles, zai gayyace shi.

Yanzu dai fitaccen dan wasan, wanda yanzu yake Kungiyar Kano Pillars, ya samu shiga cikin jerin ’yan wasa na farko da kocin ya fitar.

Ahmed Musa dai ya buga wa Nijeriya kwallo sau 110, inda ya fi kowane ɗan ƙwallo wakiltar ƙasar.

A yanzu dai tawagar ta Super Eagles tana mataki na 5 da maki 3 ne a Rukunin C, lamarin da ya sa take neman nasara a wasanninta da Rwanda da kuma Zimbabwe, don samun gurbi a Gasar Kofin Duniya da za a yi a baɗi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kofin Duniya: ’Yan wasan cikin gida 8 da Super Eagles ta gayyata
  • Iran ta kuduri aniyar yin hadin gwiwa da hukumar IAEA
  • Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaba Tinubu
  • Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaban Tinubu
  • CORET Za Ta Samar da Ayyuka 3,000 Ga Matasa A Jihohin Kaduna Da Jigawa
  • An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa
  • Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci
  • HOTUNA: NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye a cikin carbi da takalma
  • Hasashen Samun Ruwan Sama A 2025: Shawarwarin Da Kwararru Suka Bai Wa Manoma