HausaTv:
2025-03-18@14:24:28 GMT

HKI Ta Nuna Damuwarta Da Jibge Sojojin Da Gwamnatin Masar Ta Yi A Yankin Sina

Published: 18th, March 2025 GMT

Gwamnatin HKI ta bayyana damuwarta da jibge sojojin da gwamnatin kasar masar take yi a yankin Sinaa kusa da kan iyakar kasar da HKI.

Tun bayan da gwamnatin HKI ta gama lalata makaman gwamnatin kasar Siriya bayan ta taimaka ta kawo dan Daesh kan kujerar shugabancin kasar ta Siriya, kuma ta bayyana cewa yankunan da ta mamaye a kasar Siriya sun zama HKI ne har abada.

take nuna damuwa da kasar Masar.

Banda haka mun ga yadda sabon shugaban kasar ta Siriya  Julani ya yi shiri da bakinsa a kan mamayar da HKI takewa kasar Siriya da kuma yadda ta kai hare-hare fiye da dubu guda kan kasar tana lalata makamanta, ko wa ya fahinci cewa, siriya ta gama yawo,. Kuma ba zata taba daga ko tsinke a gaban HKI ba.

Tashar talabijin ta Presstv ba ce, a halin yanzu hankalin yahudawa ya koma kan kasar Masar, wacce take ganin bangare na HKI kuma kasar tana iya zama matsala gareta, duk tare da nasarorin da ta samu ya zuwa yanzu na mamayar kasashen larabawa.

Tsohon babban haffsan sojojin HKI Herzi Halevi ya fito fili ya na cewa suna cikin damuwa dangane da kasar Masar. Don ta sami ci gaba sosai a bangaren mallakan makamai  na zamani.

Ya kuma kara da cewa, a shekara ta 2011 da aka yi juyin juya halin na yanuwa musulmi, wato Muhammad Mursi sun ji tsaro, amma sun dan numfasa bayan an kauda Mursi. Sai dai a halin yanza akwai barazana na kara karfi a bangaren kasar ta  Masar, musamman bayan yakin 7 ga watan Octoba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Masar

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Sudan sun sanar da samun gagarumin ci gaba a tsakiyar Khartoum

Rundunar sojojin kasar Sudan (SAF) ta sanar da cewa, dakarunta sun samu ci gaba sosai a yakin da suke yi a babban birnin kasar Khartoum.

Mai magana da yawun rundunar sojin ta SAF, Nabil Abdalla ne ya fito fili ya bayyana cewa “Dakarunmu sun samu ci gaba sosai a tsakiyar birnin Khartoum.”

Sai dai kuma kungiyar ‘yan tawaye ta (RSF) ta musanta hakan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Sudan sun sanar da samun gagarumin ci gaba a tsakiyar Khartoum
  • Gwamnatin Kano Ta Umarci Ma’aikatanta Da Su Tantance Allbashin Watan Maris Kafin A Biya Su
  • Me Ya Sa Ba Za a Ba Yankin Taiwan Damar Samun ‘Yancin Kai Ba?
  • An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa
  • Malaman Da Aka Dakatar 207, Sun Mika Takardar Neman Afuwa Ga Gwamnatin Zamfara
  • Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza
  • Jami’ar Gwamnatin Tarayya Kachia Ta Shirya Tsaf Domin Fara Aiki
  • Nijar ta kori wasu kamfanonin China 3 daga ƙasar
  • Gwamnatin Trump na tunanin hana ‘yan kasashe kusan 40 ciki har da Iran shiga Amurka