Shugaban Putin Na Kasar Rasha Zai Zanta Ta Wayar Tarho Da Tokwaransa Na Kasar Amurka Donal Trump
Published: 18th, March 2025 GMT
A yau Talata ce ake saran shugaban kasar Rasha Vladimir Putin zai zanta ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Amurka Donal Trump, kuma wannan shine zantawar shuwagabannin kasashen biyu tun shekaru masu yawa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto kakakin Fadar Krimlin Dmitry Peskov yana fadar haka a jiya Litinin, ya kuma kara da cewa a halin yanzu ana shirye-shiryen zantawar shuwagabnnin biyu.
Peskov ya kara da cewa tattaunawar tasu zai maida hankali ne kan yakin Ukraine da matsalolin da suke kewaye da yakin.
Yau ita ce ranar da kasar Rasha ta hade yankin Cremear ga kasar Rasha, a shekara ta 2014. Kwace yankin dai ya jawo matsaloli da dama tsakanin Amurka da Rasha a lokacin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Rasha
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Ba Jakadan Afirka ta Kudu Sa’o’i 72 Ya fice daga kasar
Amurka ta baiwa jakadan Afrika ta Kudu a kasar wa’adin sa’o’i 72 na ya san idna dare ya yi masa.
Hakan dai na zuwa ne bayan da Amurkar ta ce ba ta maraba da Jakadan na Afirka ta Kudu a kasar Ebrahim Rasool.
Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya zargi jakadan da na Afrika ta Kudu da nuna “kiyayya” ga shugaban Amurka Donald Trump.
Marco Rubio ya ce Ambasada Ebrahim Rasool “yana kara ruruta wutar rikicin kabilanci kuma gwamnatin Trump ba ta da wani abin da za ta ce masa.”
Tuni Fadar shugaban kasar Afirka ta Kudu ta mayar da martani inda ta ce ta yi na’am da matakin.
Sanarwar ta ce “abin takaici ne korar jakadan na Afirka ta Kudu a Amurka” inda “ta kuduri aniyar kulla alaka mai amfani da moriyar juna” da Washington.
Rahotannin sun ce jakadan ya bayyana a wata cibiyar nazari ta Afirka ta Kudu inda ya yi ikirarin cewa yunkurin Trump na Make America Great Again, tare da tasirin Elon Musk da mataimakin shugaban kasa JD Vance, wani bangare ne na al’amuran duniya na fifita farar fata.
Dama dai dangantaka tsakanin Amurka da Afrik ata kUdu ta yi tsami sakamakon matsayin Pretoria kan hakkin Falasdinu.
Kasar Afrika ta Kudu dai ta kasance kan gaba a shari’ar da kotun kasa da kasa ta ICJ ke yi na zargin gwamnatin Isra’ila da kisan kiyashi a Gaza.
A watan da ya gabata ne dai fadar White House ta sanar da dakatar da tallafin da Amurka ke baiwa Afirka ta Kudu a matsayin martani ga karar Afirka ta Kudu da ke gaban kotun ICJ.