Janar Tsiga ya shafe kwanaki 40 a hannun masu garkuwa duk da biyan kuɗin fansa
Published: 18th, March 2025 GMT
Bayan shafe kwanaki 40 har yanzu waɗanda suka yi garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar Kula da Masu Yi wa Ƙasa Hidima ta Najeriy a(NYSC), Birgediya Janar Maharazu Tsiga mai ritaya ba su sako shi ba duk da cewa an biya kuɗin fansa.
Rahotanni sun nuna cewar an biya maƙudan kuɗaɗe don ganin an sako Janar Tsiga, wanda aka yi garkuwa da shi a ranar 5 ga watan Fabrairun da ya gabata a Ƙaramar Hukumar Bakori da ke Jihar Katsina.
Wata majiya ta kusa da iyalansa ta ce bayan kai kuɗin, sai da aka shafe mako guda kafin ’yan bindigar suka sake tuntuɓar iyalansa, inda suka haɗa su ta waya, sannan kuma suka sake neman ƙarin wasu kuɗaɗe.
“Saboda wasu dalilai gaskiya ba zan faɗi adadin kuɗin da aka biya ba amma kuɗaɗe ne masu yawan gaske,” a cewar majiyar.
Da farko dai waɗanda suka yi garkuwa da tsohon Janar ɗin, sun buƙaci a ba su naira miliyan 250 a matsayin kuɗin fansa, sai dai an ci gaba ta tattaunawa da su.
Wasu bayanai na cewa akwai yiwuwar waɗanda suka yi garkuwa da shi sun sauya masa matsugunni.
Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewacin Najeriya ACF da kuma ta Dattijan Jihar Katsina KEF, sun buƙaci gwamnatin da kuma rundunar sojojin ƙasar, su matsa ƙaimi wajen ganin an kuɓutar da shi da sauran mutanen da aka yi garkuwa tare da su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Janar Tsiga yi garkuwa da
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar haraji
Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar haraji bayan ya tsallake karatu uku a wannan Talatar.
Wannan na zuwa ne bayan karatun tsanaki da majalisar ta yi ƙudirin a ranar Alhamis ta makon jiya.
Wike ya ƙwace filin Sakatariyar PDP da ke Abuja Janar Tsiga ya shafe kwanaki 40 a hannun masu garkuwa duk da biyan kuɗin fansaAna iya tuna cewa, a makonnin bayan nan ne kwamitin kuɗi na majalisar ya gudanar da sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin, inda kuma ya tattara ra’ayoyin al’umma ya miƙa wa majalisar.
Dokar harajin da majalisar ta amince da ita ta ƙunshi ƙudiri guda huɗu da suka haɗa da ƙudirin dokar tafiyar da haraji da na kafa hukumar tattara haraji mai suna Nigeria Revenue Service da hukumar haɗaka ta tattara haraji da kuma ƙudirin haraji na Najeriya.
A watan Okotoban bara ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike da ƙudirin dokar ga majalisar dokokin ƙasar.
An dai shafe watanni ana taƙaddama kan dokar harajin wadda daga bisani gwamnonin jihohi 36 na Nijeriya suka cimma matsaya tare da amincewa da ƙudirin sabuwar dokar haraji, bayan gyare-gyaren da aka yi a kan rabon harajin kayayyaki na VAT da ya tayar da kura a ƙasar.