Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar haraji
Published: 18th, March 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar haraji bayan ya tsallake karatu uku a wannan Talatar.
Wannan na zuwa ne bayan karatun tsanaki da majalisar ta yi ƙudirin a ranar Alhamis ta makon jiya.
Wike ya ƙwace filin Sakatariyar PDP da ke Abuja Janar Tsiga ya shafe kwanaki 40 a hannun masu garkuwa duk da biyan kuɗin fansaAna iya tuna cewa, a makonnin bayan nan ne kwamitin kuɗi na majalisar ya gudanar da sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin, inda kuma ya tattara ra’ayoyin al’umma ya miƙa wa majalisar.
Dokar harajin da majalisar ta amince da ita ta ƙunshi ƙudiri guda huɗu da suka haɗa da ƙudirin dokar tafiyar da haraji da na kafa hukumar tattara haraji mai suna Nigeria Revenue Service da hukumar haɗaka ta tattara haraji da kuma ƙudirin haraji na Najeriya.
A watan Okotoban bara ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike da ƙudirin dokar ga majalisar dokokin ƙasar.
An dai shafe watanni ana taƙaddama kan dokar harajin wadda daga bisani gwamnonin jihohi 36 na Nijeriya suka cimma matsaya tare da amincewa da ƙudirin sabuwar dokar haraji, bayan gyare-gyaren da aka yi a kan rabon harajin kayayyaki na VAT da ya tayar da kura a ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Haraji Majalisar Wakilai da ƙudirin dokar dokar haraji
এছাড়াও পড়ুন:
Zaɓen 2027: Babu ɗan takarar da zai yi nasara ba tare da goyon bayan Arewa ba — Hakeem
Tsohon mashawarcin Shugaba Bola Tinubu kan harkokin siyasa, Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana cewa babu wani ɗan siyasa da zai iya lashe kujerar shugabancin Nijeriya a Zaɓen 2027 ba tare da goyon bayan yankin Arewacin ƙasar ba.
Hakeem Baba-Ahmed ya bayyana hakan a wata hira ta bidiyo tare da tsohon Babban Sakataren Hukumar Kula da Inshorar Lafiya (NHIS), Farfesa Usman Yusuf.
NDLEA ta kama hodar iblis da aka ɓoye cikin littafai ana shirin kaiwa Saudiyya Zaɓen 2027: Me ya sa jam’iyyu ke neman tabarrakin Buhari?Ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba yankin Arewacin Nijeriya zai fuskanci alƙiblarsa ta siyasa.
“Nan da watanni shida mutanen Arewacin Nijeriya za su fayyace inda suka dosa, saboda haka zaɓi ya rage wa mutanen sauran yankunan ƙasar.
“Sai dai abin da muka sani ƙarara shi ne babu wanda zai zama shugaban Nijeriya ba tare da goyon bayan Arewa ba.
Ya bayyana damuwa kan yanayin da aka tsinci kai a ƙasar a halin yanzu, inda ya buƙaci ’yan Arewa da su guji faɗa wa tarkon ’yan siyasa mayaudara a zaɓen da ke tafe.
“Muna so a samu gwamnatin da ta fahimci matsalolinmu kuma wadda za ta iya magance su.
“Bayan shekaru takwas da Buhari ya yi a karagar mulki mun ƙara buɗe ido. A yanzu wata gwamnatin ce amma har yanzu kuka muke yi. Shikenan kullum a kuka za mu ƙare?
Kazalika, Baba-Ahmed ya bayyana yadda yankin Arewa ya tagayyara a sakamakon rikicin Boko Haram wanda ya taɓa duk mabiya addinai, lamarin da ya jaddada muhimmancin haɗin kai.
“Mun dawo daga rakiyar yaudarar da ake yi mana ta zaɓen ɗan takara saboda ƙabilanci ko addini. Yanzu an rufe wannan babi.
“Yanzu abin da kawai muke buƙata shi ne shugaba nagari wanda zai magance matsalolin da muke fama da su,” in ji shi.