Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-baci a Jihar Rivers, inda ya dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, da mataimakiyarsa Ngozi Odu, da dukkan mambobin Majalisar Dokokin Jihar na tsawon watanni shida.

A wani jawabi da ya yi  ga alummar kasa ta kafafen yada labarai a ranar Talata, Shugaban kasan ya bayyana cewa an dauki wannan matakin ne sakamakon rikicin siyasa wanda ya ki ci ya ki cinyewa  a jihar, ya kuma hana gudanar da gwamnati yadda ya kamata kuma ya tauye wa jama’ar Jihar Rivers morar romon  dimokuradiyya.

Shugaban kasan ya nuna damuwarsa kan “mummunan hali” da jihar ke ciki, wanda ya kara muni bayan rushewar ginin Majalisar Dokokin Jihar da gwamnan ya yi a ranar 13 ga watan Disambar 2023. A cewarsa, duk da kokarin da ‘yan Najeriya masu kishin kasa suka yi don samun sulhu, rikicin ya ci gaba da tsananta.

Da yake magana kan hukuncin Kotun Koli na ranar 28 ga Fabrairu, 2025, wanda ya zargi gwamnan da aikata ayyukan da suka saɓa wa kundin tsarin mulki da raina doka, Shugaban kasa ya ce, “Babu gwamnati a Jihar Rivers, domin bangaren zartarwa ya rushe majalisar dokoki kuma yana mulki tamkar  mulkin danniya.”

Shugaban kasan ya kuma bayyana cewa ya samu rahotannin tsaro da ke nuna barazana ga kadarorin kasa, ciki har da lalata bututun mai da wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu biyayya  ga gwamnan ne suka aikata, ba tare da daukar wani mataki  don dakile su ba.

Shugaban kasan ya nada tsohon Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Ibokette Ibas (Rtd), a matsayin mai kula da harkokin Jihar Rivers. Ya bayyana cewa bangaren shari’a na jihar zai ci gaba da aiki kamar yadda ya saba, sannan sabon mai kula da jihar zai kasance yana tsara dokoki ne kawai da amincewar Majalisar Zartarwa ta Tarayya.

Shugaban kasan ya nuna fatan cewa wannan mataki zai tilasta dukkan bangarorin da abin ya shafa a Jihar Rivers su bi dokokin mulki tare da dawo da zaman lafiya.

Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Baci Shugaban kasan ya Jihar Rivers

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Alhazan Jihar Jigawa Ta Ware Kujeru 54 Ga Malamai Da Jami’an Kananan Hukumomi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujeru 54 na Hajj ga malamai da jami’an da za su jagoranci Alhazai don aikin Hajjin 2025.

Babban Daraktan hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga wakilin Radio Nigeria a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujerun ne domin bai wa jami’ai  da malamai damar jagorantar Alhzan jihar a Najeriya da Saudiyya.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, wannan tsari da hukumar ta kirkiro shi ne irinsa na farko a tarihin Jihar Jigawa.

 

Ya bayyana cewa, an zabi jami’an da malamai maza da mata daga  daga kananan hukumomi 27 na jihar bisa cancanta.

Ya jaddada cewa, an zaɓi mutum biyu daga kowace karamar hukuma ta jihar.

Babban Daraktan ya bayyana cewa,  malamai da jami’an sun samu umarni don koyar da maniyyata game da wajiban Hajj, ka’idoji da kuma manyan ginshiƙan aikin Hajj domin su san yadda za su gudanar da ibadar Hajj yadda ya kamata.

 

Ya bayyana cewa, bayar da cikakken horo da ilimantar da maniyyata zai taimaka musu wajen gudanar da Hajj bisa koyarwar addinin Musulunci tare da wakiltar Najeriya da kyau.

Ya ƙara da cewa, za a ci gaba da gudanar da bita ga maniyyatan Hajj na 2025 a dukkan cibiyoyin da aka kebe bayan Ramadan.

Ahmed Labbo ya ce, hukumar za ta fara raba kayayyakin tafiya ga maniyyatan Hajj na 2025 nan ba da daɗewa ba.

A cewarsa, rarraba kayayyakin tafiya wadanda suka  haɗa da yunifom da jakunkuna zai fara nan gaba a hedkwatar hukumar da wasu cibiyoyi da aka ware a faɗin kananan hukumomi 27 na jihar.

Ya bayyana cewa, jirgin farko na jigilar maniyyatan jihar zai tashi a  watan Mayu 2025 kamar yadda Hukumar Hajj ta Kasa (NAHCON) ta tsara.

Labbo ya jaddada cewa, NAHCON ta ba Max Air damar jigilar maniyyatan jihar zuwa Saudiyya ta filin jirgin sama na Nuhu Muhammadu Sunusi International Airport.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan ya gode wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.

 

USMAN MUHAMMAD ZARIA 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas
  • Tinubu ya sanya dokar ta-baci a Ribas
  • Gidauniyar Dangote Ta Bai Wa Jihar Bauchi Tallafin Buhun shinkafa 25,000
  • An Ware Sama Da Naira Biliyan 1.5 Don Fara Aiki A Sabon Kamfanin Injinan Noma Na Jigawa
  • Hukumar Alhazan Jihar Jigawa Ta Ware Kujeru 54 Ga Malamai Da Jami’an Kananan Hukumomi
  • Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaba Tinubu
  • Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaban Tinubu
  • Majalisar Ribas ta soma shirye-shiryen tsige Gwamna Fubara
  • Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci