Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-baci a Jihar Rivers, inda ya dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, da mataimakiyarsa Ngozi Odu, da dukkan mambobin Majalisar Dokokin Jihar na tsawon watanni shida.

A wani jawabi da ya yi  ga alummar kasa ta kafafen yada labarai a ranar Talata, Shugaban kasan ya bayyana cewa an dauki wannan matakin ne sakamakon rikicin siyasa wanda ya ki ci ya ki cinyewa  a jihar, ya kuma hana gudanar da gwamnati yadda ya kamata kuma ya tauye wa jama’ar Jihar Rivers morar romon  dimokuradiyya.

Shugaban kasan ya nuna damuwarsa kan “mummunan hali” da jihar ke ciki, wanda ya kara muni bayan rushewar ginin Majalisar Dokokin Jihar da gwamnan ya yi a ranar 13 ga watan Disambar 2023. A cewarsa, duk da kokarin da ‘yan Najeriya masu kishin kasa suka yi don samun sulhu, rikicin ya ci gaba da tsananta.

Da yake magana kan hukuncin Kotun Koli na ranar 28 ga Fabrairu, 2025, wanda ya zargi gwamnan da aikata ayyukan da suka saɓa wa kundin tsarin mulki da raina doka, Shugaban kasa ya ce, “Babu gwamnati a Jihar Rivers, domin bangaren zartarwa ya rushe majalisar dokoki kuma yana mulki tamkar  mulkin danniya.”

Shugaban kasan ya kuma bayyana cewa ya samu rahotannin tsaro da ke nuna barazana ga kadarorin kasa, ciki har da lalata bututun mai da wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu biyayya  ga gwamnan ne suka aikata, ba tare da daukar wani mataki  don dakile su ba.

Shugaban kasan ya nada tsohon Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Ibokette Ibas (Rtd), a matsayin mai kula da harkokin Jihar Rivers. Ya bayyana cewa bangaren shari’a na jihar zai ci gaba da aiki kamar yadda ya saba, sannan sabon mai kula da jihar zai kasance yana tsara dokoki ne kawai da amincewar Majalisar Zartarwa ta Tarayya.

Shugaban kasan ya nuna fatan cewa wannan mataki zai tilasta dukkan bangarorin da abin ya shafa a Jihar Rivers su bi dokokin mulki tare da dawo da zaman lafiya.

Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Baci Shugaban kasan ya Jihar Rivers

এছাড়াও পড়ুন:

An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo

Jami’an tsaron Jihar Edo sun sake kama wasu mafarauta hudu daga Kano, makonni kadan bayan kisan gilla da ’yan bangar Jihar Edo suka yi wa ayarin wasu mafarauta 16 daga jihar Kano a jihar.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Edo, ta ce mafarautan da aka kama sun fito ne daga Karamar Hukumar Doguwa ta Jihar Kano, kuma suna dauke da bindigogin toka guda uku, da adduna da wukake a lokacin da aka kama su.

Kakakin ’yan sanda an jihar, CSP Moses Yamu, ya ce kanawan da aka kama mafarauta ne ba kamar yadda ake yadawa a kafofin sada zumunta cewa makiyaya ba ne.

Ya bayyana cewa jami’an kungiyar tsaro ta Jhar Edo ne suka kama mafarautan sannan suka damka su ga ’yan sanda inda ake yi musu tambayoyi a ofishin ’yan sanda da ke yankin Ikpoba Hill.

’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu

Ya ce an, “An kama mafarautan da suka fito daga Karamar Hukumar Doguwa ta Jihar Kano a yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa yankin Uvbe da ke Karamar Hukumar Orhionwon a Jihar Edo. A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike.”

Da haka Kwamishinan ’yan sandan jihar, Monday Agbonika, ya gargadi jama’ar jihar da su guji yada abin da ba gaskiya ba ne game da lamarin, domin yana iya tayar da zaune tsaye.

Idan ba a manta ba, a cikin watan Ramadan, gab Sallah Karama ne ’yan banga suka yi wa wasu mafarauta 16 daga Jihar Kano da ke hanyarsu ta komawa gida hutun sallah kisan gilla a yankin Uromi da ke jihar, lamarin da ya haifar da tayar da jijiyoyin wuya, inda har yanzu ake kokarin shawo kansa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
  • ‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Mamaye Sassan Jihar Borno -Zulum