Aminiya:
2025-03-18@22:38:04 GMT

An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas

Published: 19th, March 2025 GMT

Mazauna sun shiga zaman ɗar-ɗar a yayin da motocin yaƙi na sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Jihar Ribas.

Wannan dai na zuwa ne jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar.

Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau Tinubu ya sanya dokar ta-baci a Jihar Ribas

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa fiye da motocin soji 10 aka hanga suna sintiri a kan hanyar zuwa gidan gwamnatin yayin da wasu motocin yaƙi masu sulke suka tsaya wuri-wuri a hanyar.

Majiyar ta ce titunan birnin na Fatakwal sun zama fayau a yayin da mazauna suka tsere gidajensu.

Babu tabbaci ko gwamnan da aka dakatar, Similanayi Fubara yana cikin gidan gwamnatin a halin yanzu.

Sai dai majiyoyi sun ce akwai yiwuwar gwamnan ya samu labarin cewa za a ayyana dokar ta ɓacin tun kafin faruwar lamarin.

Bayanai sun ce gwamnan ya shafe tsawon wunin wannan rana ta Talata yana ganawa da ’yan majalisar zartarwarsa.

A halin yanzu dai birnin na Fatakwal ya zama fayau a yayin mazauna da ’yan kasuwa duk sun koma gidajensu.

Dalilin da Tinubu ya ayyana dokar ta ɓacin

Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas bayan rikita-rikitar siyasa da jihar ta daɗe tana fama da shi tare da kuma da naɗa wanda zai riƙe muƙamin gwamnan jihar na tsawon wata shida.

Tinubu ya sanar da matakin ne a wani jawabi da ya yi ta kafafen talabijin na ƙasar da yammacin ranar Talata.

A cikin jawabin nasa, Tinubu ya yi nuni da yadda aka rushe ginin majalisar dokokin jihar watanni 18 da suka gabata, wadda aka kasa sake gina ta har zuwa wannan lokaci.

“Jihar ta tsaya cik tun bayan ɓarkewar rikicin siyasar inda aka tauye wa al’ummar jihar hakkinsu na cin moriyar mulkin dimokuraɗiyya.

“Na yi iyakar bakin ƙoƙarina wajen ganin yadda za a magance matsalar to amma duka ɓangarorin sun yi watsi da yunkurin.

“Bayan nazari kan halin da ake ciki a jihar Rivers, ya zama wajibi na yi amfani da sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999.

“A kan haka, na ayyana dokar ta-ɓaci daga yau 18 ga watan Maris, 2025.

“Da wannan bayani, gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Mrs Ngozi Odu da kuma dukkanin zaɓaɓbun ƴanmajalisar dokokin Jihar Ribas, an dakatar da su na wata shida, a matakin farko.

“A halin yanzu, na naɗa Vice Admiral Ibokette Ibas a matsayin wanda zai gudanar da lamurran jihar, domin amfanin al’ummar jihar,” in ji Tinubu.

Sai dai a cikin jawabin nasa, Tinubu ya bayyana cewa wannan doka da ya ƙaƙaba ba ta shafi ɓangaren shari’a na jihar ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Jihar Ribas Siminalayi Fubara a ayyana dokar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe ’yan bindiga 31 tare da lalata sansaninsu a Jihar Katsina, yayin wasu hare-hare guda biyu da suka kai.

A farmaki na farko, dakarun Operation Fansan Yamma sun yi artabu da ’yan bindiga a garin Maigora da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.

Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka

Da farko, sojojin sun kashe ’yan bindiga biyar bayan sun kai farmaki garin.

Sai dai lokacin da suka sake haɗuwa don kai harin ramuwar gayya, sojojin sun sake kashe guda bakwai, ciki har da Dogo, wanda babban Kwamanda ne a cikinsu.

Haka kuma, sojojin sun ƙwace babura guda bakwai da ‘yan bindigar ke amfani da su.

A wani farmakin, rundunar sojojin sama ta yi luguden wuta a maboyar ’yan bindiga da ke dajin Unguwar Goga, Ruwan Godiya, a Ƙaramar Hukumar Faskari.

Sun lalata sansanin shugabannin ’yan bindiga biyu; Alhaji Gero da Alhaji Riga, inda suka kashe aƙalla mahara 19.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa sojojin Najeriya na ƙara ƙaimi wajen murƙushe ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma, tare da lalata sansaninsu.

Har ila yau, sojojin na ci gaba da sintiri ta sama da ƙasa don daƙile yunƙurin ’yan bindiga na sake hare-hare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Dakatar Da Gwamnan Jihar Rivers Da ‘Yan Majalisar Dokokin Jihar
  • Tinubu ya sanya dokar ta-baci a Ribas
  • Gidauniyar Dangote Ta Bai Wa Jihar Bauchi Tallafin Buhun shinkafa 25,000
  • Majalisar Ribas ta soma shirye-shiryen tsige Gwamna Fubara
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina
  • Cikar FRCN Kaduna Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon
  • Cikar FRCN Shekaru 63: An Bukaci Gwamnonin Jihohin Arewa Su Tabbatar Da Dorewar Gidan Rediyon
  • Abba ya mayar da filin Idi cibiyar harkokin addinin Musulunci