Sashen Masana’antun Dijital Na Kasar Sin Ya Samu Karin Riba Da Ci Gaba A Shekarar 2024
Published: 19th, March 2025 GMT
Alkaluma daga ma’aikatar masana’antu da fasahar sadarwa ta kasar Sin ko MIIT, sun nuna irin ci gaba bisa daidaito da sashen masana’antun dijital na kasar Sin ya samu a shekarar 2024 da ta gabata, inda a shekarar ta bara sashen ya samu karin kudin shiga da riba.
Alkaluman da MIIT ta fitar a jiya Litinin, sun nuna a baran, sashen ya kudin da ya kai kudin Sin yuan tiriliyan 35, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 4.
Bugu da kari, a shekarar ta 2024, karin kimar hajoji da manyan masana’antun kirar na’urori masu kwakwalwa ke samarwa, da na na’urorin sadarwa da sauran kayayyakin laturoni, ya karu da kaso 11.8 bisa dari, karin da ya kai na kaso 8.4 bisa dari kan na shekarar da ta gabace ta.
Fannin samar da manhajoji na kasar, shi ma ya samar da karin ribar kaso 10 bisa dari, inda darajarsa ta kai tiriliyan 13.7. Ana kuma danganta ci gaban fannin da fadadar sashen fasahohin kirkirarriyar basira ko AI, da dandalolin adana bayanai, da sauran sassan hada hadar kasuwanci masu alaka da shi. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ministan Noma Na Gambiya: Hadin Kan Gambiya Da Sin A Fannin Aikin Gona Ya Haifar Da Sakamako Mai Kyau
Ministan noma na kasar Gambiya Demba Sabally ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a kwanan baya cewa, goyon baya da taimakon fasaha na kasar Sin sun taka muhimmiyar rawa wajen samar da gagarumin ci gaba a fannin aikin gona na Gambiya a shekarun baya-bayan nan.
Ministan ya ce, yawan amfanin gona da kasar ta Gambiya ke samu na ci gaba da karuwa, inda yawan shinkafar da kasar ta samar ya haura tan 48,000 a shekarar 2024, wanda ya kafa tarihi. Sabally ya kuma bayyana cewa, kirkire-kirkire a fannin samar da ababen more rayuwa, da fasahohin aikin gona masu yawan gaske da tawagogin kasar Sin suka yi amfani da su, sun taka rawa wajen kai wa ga wannan matsayi.
Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (3) Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar ‘Yan MajalisuYana mai cewa, tawagar kwararrun kasar Sin sun ba da taimako a kasar Gambiya ta hanyar gabatar da nau’o’in shinkafa masu inganci da suka hada da ire-iren da aka tagwaita da masu samar da girbi mai yawa, wadanda ke da matukar muhimmanci ga bunkasa aikin gonar Gambiya.
Sabally ya kammala da cewa, Gambiya za ta ci gaba da tura ma’aikatan aikin gona zuwa kasar Sin don samun horo mai zurfi, kuma yana fatan zurfafa hadin gwiwa a tsakanin kasarsa da Sin a fannin aikin gona, da sabbin fasahohi, da bunkasa hazaka. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp